• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Mutane 16 Da Ake Zargi Da Satar Mai A Ribas

by Sadiq
3 years ago
Cafke

Hukumar tsaron farin kaya ta Nijeriya (NSCDC) a Jihar Ribas a ranar Talata ta gabatar da wasu mutane 16 da ake zargin barayin mai ne da laifin tace danyen mai ba bisa ka’ida ba domin samar da dizal.

Kwamandan rundunar ‘yansandan jihar, Mista Michael Ogar, ya gurfanar da mutanen 16 a gaban manema labarai a Fatakwal.

  •  Majalisar Dokokin Kano Ta Amince A Sauya Sunan Jami’ar KUST Zuwa Sunan Dangote
  • Maulidi: Kungiyoyin Mata Sun Yi Taro Kan Muhimmanci Koyi Da Fiyayyen Halitta SAW A Abuja

Ya ce jami’an NSCDC da na ruwa na Nijeriya sun kama su ne a wani samame daban-daban a wurare daban-daban a jihar.

A cewarsa, sun kwace kimanin lita 200,000 na gurbataccen dizal da ake shirin rabawa masu ababen hawa a jihar.

“Takwas daga cikin wadanda ake zargin jami’an NSCDC na sashin yaki da barna ne suka kama su yayin da sauran takwas din kuma sojojin ruwa na Nijeriya da ke Fatakwal ne suka mika mana su.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

“An kama mutane 16 da ake zargin suna da hannu wajen satar mai da kuma tace man dizal ba bisa ka’ida ba.

“An kama wasu daga cikin wadanda ake zargin sun kwashe kimanin lita 200,000 na dizal tare da manyan motocinsu, motocin wasanni da sauran motoci zuwa wurare daban-daban a cikin jihar kafin a kama su,” in ji shi.

Ogar ya ce rundunar ta kama wasu da dama tare da kwace albarkatun man fetur biyo bayan umarnin da ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola da Gwamna Nyesom Wike na Ribas suka yi bai NSCDC.

Ya kuma tabbatar wa da jama’a cewa, rundunar ba za ta huta ba har sai an dakatar da duk wani nau’i na fasa kwaurin man fetur ba bisa ka’ida ba da barnata ayyukan man fetur da iskar gas a jihar.

“Ba za mu yi sulhu a kan aikinmu ba. Yawan kama su na nuna cewa jami’anmu da mutanenmu suna bin umarnin gwamnati na dakatar da barnace-barnace.

“Baya ga wannan, muna kuma bin masu gidajen mai da ke hada baki da masu aikata laifuka ta hanyar ba su damar amfani da gine-ginensu da kayan aikinsu wajen tara man fetur ba bisa ka’ida ba.

Ya kara da cewa, “Rundunar ta tana bin irin wadannan masu gidajen man, kuma za ta kama su tare da gurfanar da su a gaban kuliya saboda sun bari an yi amfani da kadarorinsu wajen aikata haramtattun ayyuka.”

Kwamandan ya ce nan ba da jimawa ba za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kuliya yayin da rundunar za ta nemi gwamnatin tarayya ta kwace motocin da man fetur din da ta kama.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
Manyan Labarai

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya
Labarai

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Yi Barazanar Aure ‘Ya’yan Tsohon Akanta-Janar Na Zamfara Da Suka Sace

'Yan Bindiga Sun Yi Barazanar Aure 'Ya'yan Tsohon Akanta-Janar Na Zamfara Da Suka Sace

LABARAI MASU NASABA

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.