ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Mutane 16 Da Ake Zargi Da Satar Mai A Ribas

by Sadiq
4 years ago
Cafke

Hukumar tsaron farin kaya ta Nijeriya (NSCDC) a Jihar Ribas a ranar Talata ta gabatar da wasu mutane 16 da ake zargin barayin mai ne da laifin tace danyen mai ba bisa ka’ida ba domin samar da dizal.

Kwamandan rundunar ‘yansandan jihar, Mista Michael Ogar, ya gurfanar da mutanen 16 a gaban manema labarai a Fatakwal.

  •  Majalisar Dokokin Kano Ta Amince A Sauya Sunan Jami’ar KUST Zuwa Sunan Dangote
  • Maulidi: Kungiyoyin Mata Sun Yi Taro Kan Muhimmanci Koyi Da Fiyayyen Halitta SAW A Abuja

Ya ce jami’an NSCDC da na ruwa na Nijeriya sun kama su ne a wani samame daban-daban a wurare daban-daban a jihar.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, sun kwace kimanin lita 200,000 na gurbataccen dizal da ake shirin rabawa masu ababen hawa a jihar.

“Takwas daga cikin wadanda ake zargin jami’an NSCDC na sashin yaki da barna ne suka kama su yayin da sauran takwas din kuma sojojin ruwa na Nijeriya da ke Fatakwal ne suka mika mana su.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

“An kama mutane 16 da ake zargin suna da hannu wajen satar mai da kuma tace man dizal ba bisa ka’ida ba.

“An kama wasu daga cikin wadanda ake zargin sun kwashe kimanin lita 200,000 na dizal tare da manyan motocinsu, motocin wasanni da sauran motoci zuwa wurare daban-daban a cikin jihar kafin a kama su,” in ji shi.

Ogar ya ce rundunar ta kama wasu da dama tare da kwace albarkatun man fetur biyo bayan umarnin da ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola da Gwamna Nyesom Wike na Ribas suka yi bai NSCDC.

Ya kuma tabbatar wa da jama’a cewa, rundunar ba za ta huta ba har sai an dakatar da duk wani nau’i na fasa kwaurin man fetur ba bisa ka’ida ba da barnata ayyukan man fetur da iskar gas a jihar.

“Ba za mu yi sulhu a kan aikinmu ba. Yawan kama su na nuna cewa jami’anmu da mutanenmu suna bin umarnin gwamnati na dakatar da barnace-barnace.

“Baya ga wannan, muna kuma bin masu gidajen mai da ke hada baki da masu aikata laifuka ta hanyar ba su damar amfani da gine-ginensu da kayan aikinsu wajen tara man fetur ba bisa ka’ida ba.

Ya kara da cewa, “Rundunar ta tana bin irin wadannan masu gidajen man, kuma za ta kama su tare da gurfanar da su a gaban kuliya saboda sun bari an yi amfani da kadarorinsu wajen aikata haramtattun ayyuka.”

Kwamandan ya ce nan ba da jimawa ba za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kuliya yayin da rundunar za ta nemi gwamnatin tarayya ta kwace motocin da man fetur din da ta kama.

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo
Labarai

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Yi Barazanar Aure ‘Ya’yan Tsohon Akanta-Janar Na Zamfara Da Suka Sace

'Yan Bindiga Sun Yi Barazanar Aure 'Ya'yan Tsohon Akanta-Janar Na Zamfara Da Suka Sace

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.