ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Mutane 16 Da Ake Zargi Da Satar Mai A Ribas

by Sadiq
4 years ago
Cafke

Hukumar tsaron farin kaya ta Nijeriya (NSCDC) a Jihar Ribas a ranar Talata ta gabatar da wasu mutane 16 da ake zargin barayin mai ne da laifin tace danyen mai ba bisa ka’ida ba domin samar da dizal.

Kwamandan rundunar ‘yansandan jihar, Mista Michael Ogar, ya gurfanar da mutanen 16 a gaban manema labarai a Fatakwal.

  •  Majalisar Dokokin Kano Ta Amince A Sauya Sunan Jami’ar KUST Zuwa Sunan Dangote
  • Maulidi: Kungiyoyin Mata Sun Yi Taro Kan Muhimmanci Koyi Da Fiyayyen Halitta SAW A Abuja

Ya ce jami’an NSCDC da na ruwa na Nijeriya sun kama su ne a wani samame daban-daban a wurare daban-daban a jihar.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, sun kwace kimanin lita 200,000 na gurbataccen dizal da ake shirin rabawa masu ababen hawa a jihar.

“Takwas daga cikin wadanda ake zargin jami’an NSCDC na sashin yaki da barna ne suka kama su yayin da sauran takwas din kuma sojojin ruwa na Nijeriya da ke Fatakwal ne suka mika mana su.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

“An kama mutane 16 da ake zargin suna da hannu wajen satar mai da kuma tace man dizal ba bisa ka’ida ba.

“An kama wasu daga cikin wadanda ake zargin sun kwashe kimanin lita 200,000 na dizal tare da manyan motocinsu, motocin wasanni da sauran motoci zuwa wurare daban-daban a cikin jihar kafin a kama su,” in ji shi.

Ogar ya ce rundunar ta kama wasu da dama tare da kwace albarkatun man fetur biyo bayan umarnin da ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola da Gwamna Nyesom Wike na Ribas suka yi bai NSCDC.

Ya kuma tabbatar wa da jama’a cewa, rundunar ba za ta huta ba har sai an dakatar da duk wani nau’i na fasa kwaurin man fetur ba bisa ka’ida ba da barnata ayyukan man fetur da iskar gas a jihar.

“Ba za mu yi sulhu a kan aikinmu ba. Yawan kama su na nuna cewa jami’anmu da mutanenmu suna bin umarnin gwamnati na dakatar da barnace-barnace.

“Baya ga wannan, muna kuma bin masu gidajen mai da ke hada baki da masu aikata laifuka ta hanyar ba su damar amfani da gine-ginensu da kayan aikinsu wajen tara man fetur ba bisa ka’ida ba.

Ya kara da cewa, “Rundunar ta tana bin irin wadannan masu gidajen man, kuma za ta kama su tare da gurfanar da su a gaban kuliya saboda sun bari an yi amfani da kadarorinsu wajen aikata haramtattun ayyuka.”

Kwamandan ya ce nan ba da jimawa ba za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kuliya yayin da rundunar za ta nemi gwamnatin tarayya ta kwace motocin da man fetur din da ta kama.

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Yi Barazanar Aure ‘Ya’yan Tsohon Akanta-Janar Na Zamfara Da Suka Sace

'Yan Bindiga Sun Yi Barazanar Aure 'Ya'yan Tsohon Akanta-Janar Na Zamfara Da Suka Sace

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.