ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Mutane 16 Da Ake Zargi Da Satar Mai A Ribas

by Sadiq
4 years ago
Cafke

Hukumar tsaron farin kaya ta Nijeriya (NSCDC) a Jihar Ribas a ranar Talata ta gabatar da wasu mutane 16 da ake zargin barayin mai ne da laifin tace danyen mai ba bisa ka’ida ba domin samar da dizal.

Kwamandan rundunar ‘yansandan jihar, Mista Michael Ogar, ya gurfanar da mutanen 16 a gaban manema labarai a Fatakwal.

  •  Majalisar Dokokin Kano Ta Amince A Sauya Sunan Jami’ar KUST Zuwa Sunan Dangote
  • Maulidi: Kungiyoyin Mata Sun Yi Taro Kan Muhimmanci Koyi Da Fiyayyen Halitta SAW A Abuja

Ya ce jami’an NSCDC da na ruwa na Nijeriya sun kama su ne a wani samame daban-daban a wurare daban-daban a jihar.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, sun kwace kimanin lita 200,000 na gurbataccen dizal da ake shirin rabawa masu ababen hawa a jihar.

“Takwas daga cikin wadanda ake zargin jami’an NSCDC na sashin yaki da barna ne suka kama su yayin da sauran takwas din kuma sojojin ruwa na Nijeriya da ke Fatakwal ne suka mika mana su.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“An kama mutane 16 da ake zargin suna da hannu wajen satar mai da kuma tace man dizal ba bisa ka’ida ba.

“An kama wasu daga cikin wadanda ake zargin sun kwashe kimanin lita 200,000 na dizal tare da manyan motocinsu, motocin wasanni da sauran motoci zuwa wurare daban-daban a cikin jihar kafin a kama su,” in ji shi.

Ogar ya ce rundunar ta kama wasu da dama tare da kwace albarkatun man fetur biyo bayan umarnin da ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola da Gwamna Nyesom Wike na Ribas suka yi bai NSCDC.

Ya kuma tabbatar wa da jama’a cewa, rundunar ba za ta huta ba har sai an dakatar da duk wani nau’i na fasa kwaurin man fetur ba bisa ka’ida ba da barnata ayyukan man fetur da iskar gas a jihar.

“Ba za mu yi sulhu a kan aikinmu ba. Yawan kama su na nuna cewa jami’anmu da mutanenmu suna bin umarnin gwamnati na dakatar da barnace-barnace.

“Baya ga wannan, muna kuma bin masu gidajen mai da ke hada baki da masu aikata laifuka ta hanyar ba su damar amfani da gine-ginensu da kayan aikinsu wajen tara man fetur ba bisa ka’ida ba.

Ya kara da cewa, “Rundunar ta tana bin irin wadannan masu gidajen man, kuma za ta kama su tare da gurfanar da su a gaban kuliya saboda sun bari an yi amfani da kadarorinsu wajen aikata haramtattun ayyuka.”

Kwamandan ya ce nan ba da jimawa ba za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kuliya yayin da rundunar za ta nemi gwamnatin tarayya ta kwace motocin da man fetur din da ta kama.

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Yi Barazanar Aure ‘Ya’yan Tsohon Akanta-Janar Na Zamfara Da Suka Sace

'Yan Bindiga Sun Yi Barazanar Aure 'Ya'yan Tsohon Akanta-Janar Na Zamfara Da Suka Sace

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.