• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Damfari ‘Yan Nijeriya Naira Biliyan 93.72 A Shekaru 2 – Bincike

by Khalid Idris Doya
10 months ago
Naira

‘Yan Nijeriya sun yi asarar sama da naira biliyan 93.72 sakamakon ayyukan zamba a tsakanin watan Janairun 2023 zuwa Disamban 2024.

Wannan ya kai ga adadin asarar sama da naira 1, 005,170,000,000 da aka tafka a cikin shekaru 25.

‘Yan damfara da masu zamba cikin aminci na ci gaba da vullo da sabbin dabaru da hanyoyin yadda za su cuci jama’a duk kuwa da yawan wayar da kan jama’a da ake yi na hanyoyin da za su bi wajen kauce wa masu irin wannan ta’asar.

  • Me Ya Sa Fursunoni Masu Jiran Hukuncin Kisa Ke Ƙara Cunkoso A Gidajen Yarin Nijeriya?
  • Abuubuwan Da Suka Fi Daukar Hankalin ‘Yan Nijeriya A 2024

A Disamban 2022, Darakta a sashin Inshura ta Nijeriya (NDIC), Michael Oladele, ya shaida yadda jama’a ke tafka dimbin asara sakamakon aikace-aikacen damfara da zamba a cikin kasar Nijeriya.

A lokacin ya shaida cewar adadin kudi naira biliyan 911.45 ne aka yi asararsu a cikin shekaru 23, inda ya ce, babu shakka asarar wannan makudan kudaden ya gurgunta tattalin arzikin wadanda lamarin ya shafa da kuma tattalin arzikin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

A watan Oktoban 2024, wani mai suna Chinedu Okoronkwo an gurfanar da shi a gaban babban kotun tarayya da ke Enugi, bisa zarginsa da ayyukan damfara ta kamfanin ‘Reliance Microfinance Cooperative Society Limited’ inda ya damfari masu zuba hannun jari naira miliyan 71.58.

Zuwa watan Oktoban 2024, harkokin damfara ya shafi ‘yan Nijeriya miliyan 2.7 da suka rasa naira biliyan 89.4 kan masu damfara ta BBHTV. Duk da kuwa gwamnatin tarayya ta kulle asusun bankunan BBHTV da dama.

Watanni biyar kacal da fara aiki, BBHTV ta sanar da wadanda abin ya shafa cewa hukumar tattara kudaden shiga ta tarayya (FIRS) ta rufe asusun ta da dama.

Masu gudanar da shirin asusun sun yi ikirarin cewa wadannan rufaffun asusu na da jimillar naira biliyan 89.4.

Sakamakon karuwar wadannan ayyukan damfara, majalisar dattawa ta zartar da dokar saka hannun jari da tsare-tsare (ISB) 2024, don maye gurbin dokar zuba jari da tsaro ta 2007, domin dakile aniyar masu zamba da damfarar mutane.

Shugaban kwamitin majalisar dattawa mai kula da harkokin manyan kasuwanci, Osita Izunaso, ya ce kudirin dokar zai kare mutuncin tabbatar da tsaro daga duk wani nau’in cin zarafin ‘yan kasuwa, kyautata tsaron kasuwanci, hana cin hanci da rashawa, haramtattu ayyuka, zamba da kuma rashin adalci a harkokin kasuwanci da suka shafi harkokin zuba jari.

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara
Labarai

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

October 30, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

October 30, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai
Labarai

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

October 30, 2025
Next Post
Gwarzon Gwamnan 2024  – Alhaji Abba Kabir Yusuf

Gwarzon Gwamnan 2024 - Alhaji Abba Kabir Yusuf

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

October 30, 2025
An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

October 30, 2025
Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

October 30, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

October 30, 2025
Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

October 30, 2025
Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

October 30, 2025
Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

October 30, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

October 30, 2025
Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

October 30, 2025
Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.