• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Damfari ‘Yan Nijeriya Naira Biliyan 93.72 A Shekaru 2 – Bincike

by Khalid Idris Doya
7 months ago
in Labarai
0
Kar A Tsammaci Amincewa Da Kasafin 2025 Kafin Ranar 31 Ga Janairu – Majalisar Dattawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan Nijeriya sun yi asarar sama da naira biliyan 93.72 sakamakon ayyukan zamba a tsakanin watan Janairun 2023 zuwa Disamban 2024.

Wannan ya kai ga adadin asarar sama da naira 1, 005,170,000,000 da aka tafka a cikin shekaru 25.

‘Yan damfara da masu zamba cikin aminci na ci gaba da vullo da sabbin dabaru da hanyoyin yadda za su cuci jama’a duk kuwa da yawan wayar da kan jama’a da ake yi na hanyoyin da za su bi wajen kauce wa masu irin wannan ta’asar.

  • Me Ya Sa Fursunoni Masu Jiran Hukuncin Kisa Ke Ƙara Cunkoso A Gidajen Yarin Nijeriya?
  • Abuubuwan Da Suka Fi Daukar Hankalin ‘Yan Nijeriya A 2024

A Disamban 2022, Darakta a sashin Inshura ta Nijeriya (NDIC), Michael Oladele, ya shaida yadda jama’a ke tafka dimbin asara sakamakon aikace-aikacen damfara da zamba a cikin kasar Nijeriya.

A lokacin ya shaida cewar adadin kudi naira biliyan 911.45 ne aka yi asararsu a cikin shekaru 23, inda ya ce, babu shakka asarar wannan makudan kudaden ya gurgunta tattalin arzikin wadanda lamarin ya shafa da kuma tattalin arzikin Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

A watan Oktoban 2024, wani mai suna Chinedu Okoronkwo an gurfanar da shi a gaban babban kotun tarayya da ke Enugi, bisa zarginsa da ayyukan damfara ta kamfanin ‘Reliance Microfinance Cooperative Society Limited’ inda ya damfari masu zuba hannun jari naira miliyan 71.58.

Zuwa watan Oktoban 2024, harkokin damfara ya shafi ‘yan Nijeriya miliyan 2.7 da suka rasa naira biliyan 89.4 kan masu damfara ta BBHTV. Duk da kuwa gwamnatin tarayya ta kulle asusun bankunan BBHTV da dama.

Watanni biyar kacal da fara aiki, BBHTV ta sanar da wadanda abin ya shafa cewa hukumar tattara kudaden shiga ta tarayya (FIRS) ta rufe asusun ta da dama.

Masu gudanar da shirin asusun sun yi ikirarin cewa wadannan rufaffun asusu na da jimillar naira biliyan 89.4.

Sakamakon karuwar wadannan ayyukan damfara, majalisar dattawa ta zartar da dokar saka hannun jari da tsare-tsare (ISB) 2024, don maye gurbin dokar zuba jari da tsaro ta 2007, domin dakile aniyar masu zamba da damfarar mutane.

Shugaban kwamitin majalisar dattawa mai kula da harkokin manyan kasuwanci, Osita Izunaso, ya ce kudirin dokar zai kare mutuncin tabbatar da tsaro daga duk wani nau’in cin zarafin ‘yan kasuwa, kyautata tsaron kasuwanci, hana cin hanci da rashawa, haramtattu ayyuka, zamba da kuma rashin adalci a harkokin kasuwanci da suka shafi harkokin zuba jari.

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

CBN Ya Ce Bai Tilasta Wa Ma’aikata 1,000 Yin Ritaya Ba

Next Post

Gwarzon Gwamnan 2024 – Alhaji Abba Kabir Yusuf

Related

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto
Labarai

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

2 hours ago
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

6 hours ago
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Labarai

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

7 hours ago
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
Labarai

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

8 hours ago
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

10 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

13 hours ago
Next Post
Gwarzon Gwamnan 2024  – Alhaji Abba Kabir Yusuf

Gwarzon Gwamnan 2024 - Alhaji Abba Kabir Yusuf

LABARAI MASU NASABA

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

August 9, 2025
Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

August 9, 2025
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

August 9, 2025
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.