ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abuubuwan Da Suka Fi Daukar Hankalin ‘Yan Nijeriya A 2024

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Hankali

Shekarar 2024 ta zo da abubwuan al’ajabi da dama  masu ban mamaki wasu kuma da ban haushi wadanda suka hadu suka sa shekarar ta zama ta musamman a cikin ‘yan shekarun nan na baya bayan nan. Mun yi nazarin vangarori da dama da suka hada da tsaro, tattalin arziki da siyasa, mu zakulo muku abubuwan da suka fi daukar hankalin al’ummar Nijeriya a cikin shekarar 2024.

Al’amura da dama sun dauki hankulan ‘yan Nijeriya, inda suka haifar da zazzafar muhawara da wayar da kan jama’a kan muhimman batutuwa a shekarar 2024. Daga ci gaban siyasar duniya zuwa sauye-sauyen manufofin gida da rikice-rikice, wadannan lokutan sun tabbatar da tsara labarin kasa, inda mutane da yawa suka rika komawa dandalin na dijital don samun bayanai.

  • Dokar Haraji Za Ta Ƙara Jefa Al’umma Cikin Talauci – Gwamnatin Kano
  • Waiwaye a Kan Wasu Labarai Mafi Muhimmanci Game Da Mashigin Tekun Yankin Taiwan a 2024 Da CMG Ya Gabatar

A zamanin da kafofin yada labarai na al’ada sukan yi ta kokarin kutsawa cikin hayaniyar yanayin da ya mamaye kafofin yada labarai, ‘yan Nijeriya sun kara karkata zuwa intanet don zurfafa bincike kan al’amuran da suka shafe su kai tsaye ko a fakaice.

ADVERTISEMENT

Kafofin sada zumunta sun fito a matsayin tashar farko don samar da bayanai na ainihi, musamman a tsakanin matasa. Ko ma dai yaya, injunan bincike na Google sun ga amfani mai mahimmanci, tare da yawancin neman sabuntawa akan batutuwan da suka mamaye kanun labarai.

Zaven shugaban kasar Amurka

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Zaven shugaban kasar Amurka na shekarar 2024 ya dauki hankulan ‘yan Nijeriya, kamar yadda aka saba yi zaven daya daga cikin kasashen da suka fi tasiri a duniya. A wannan shekara, takara tsakanin Donald Trump da Kamala Harris ta jawo hankulan jama’a musamman saboda yanayin da take da shi da kuma tasirinta a duniya.

‘Yan Nijeriya sun bi kamfen, muhawara, da sakamakon ta kafofin yada labarai da kafofin sada zumunta. Mutane da yawa sun nemi fahimtar yadda manufofin ’yan takarar, musamman kan shige da fice, za su shafi ’yan Nijeriya da ke fatan tafiya Amurka don neman ilimi, aiki, ko nishadi. A matsayinta na al’ummar da ke da alaka mai karfi da al’amuran duniya, sha’awar Nijeriya ga zavukan Amurka ya kai ga tattaunawa kan harkokin mulki, dimokuradiyya, da kuma tasirinsa ga Afirka.

Amincewa da sabon taken Nijeriya

Wani muhimmin al’amari a Nijeriya shi ne matakin da gwamnati ta dauka na maido da taken kasar na farko, wanda Lillian Jean Williams ta hada a shekarar 1959. Wannan ya nuna sauyi daga wakar da aka fara amfani da ita tun 1978, wadda Pa Benedict Odiase ya kirkira.

Komawa taken na farko wani shiri ne na gwamnati da nufin inganta hadin kan kasa da sanin ya kamata. Wannan shawarar ta haifar da tattaunawa mai yawa game da kishin kasa da kuma ci gaba da alamun diyaucin Nijeriya. Makarantu, ofisoshi, da wuraren jama’a sun daidaita ga sauyin, tare da yawancin yin tunani akan mahimmancin tarihin taken da kuma dacewarta a yau.

Lalacewar babbabar tashar wutar Lantarki ta kasa

Lalacewar babbar tashar wutar lantarki ta kasa a shekarar 2024 ya nuna irin kalubalen da ke fuskantar vangaren wutar lantarkin Nijeriya. Yawaitar katsewar ta kawo cikas ga rayuwar yau da kullum ga miliyoyin ‘yan Nijeriya, lamarin da ya shafi gidaje, kasuwanci, da muhimman ayyuka.

Wannan lamarin ya sake haifar da muhawara game da yanayin samar da makamashi na kasar da kuma bukatar samar da mafita mai dorewa. ‘Yan Nijeriya sun yi amfani da shafukan sada zumunta don bayyana takaicinsu tare da neman karin bayani, yayin da kasuwancin da suka dogara da wutar lantarki suka ba da rahoton karin farashin aiki. Lalacewar tashar wutar ta kuma nuna gaggawar saka hannun jari a vangaren makamashi mai sabuntawa da kuma sauye-sauyen tsarin don tabbatar da samar da wutar lantarki mai inganci a fadin kasar.

Karin mafi karancin albashi na kasa

Dangane da tsadar rayuwa, gwamnatin Nijeriya ta kara mafi karancin albashi daga Naira 30,000 zuwa Naira 70,000. Wannan shawarar ta biyo bayan doguwar tattaunawa tsakanin kungiyoyin kwadago da jami’an gwamnati, da kuma zanga-zangar da ma’aikata suka yi a fadin kasar.

Ana kallon karin mafi karancin albashi a matsayin matakin da ya dace don magance hauhawar farashin kayayyaki da kuma fafutukar neman kudi na ‘yan Nijeriya da dama. Koma dai yaya, an sanya damuwa game da aiwatar da shi da yuwuwar karin farashin kayayyaki da ayyukan yau da kullum. Masu daukar ma’aikata, musamman a kamfanoni masu zaman kansu, sun bayyana kalubale wajen biyan sabbin bukatu. Duk da wannan damuwar, shawarar ta yi tasiri ga ma’aikata da yawa a matsayin wani mataki na inganta rayuwa.

Fashewar bam a Ibadan

A watan Janairun 2024, an samu fashewar wani abu a Ibadan, Jihar Oyo, wanda ya jawo hankalin jama’a ga al’amuran tsaro da ka’idojin birane. Lamarin wanda ya afku a wani wuri mai dimbin jama’a, ya faru ne sakamakon bama-baman da aka ajiye a wani gida mai zaman kansa, wanda yi sanadin asarar rayuka da jikkata jama’a, tare da lalata dukiyoyi da dama.

Tawagar masu ba da agajin gaggawa da jami’an tsaro sun yi aiki kan ayyukan bincike da ceto, tare da kwashe baraguzan gine-gine da kuma taimaka wa iyalai da abin ya shafa. Fashewar ta bayyana givin da ake samu wajen aiwatar da doka da wayar da kan al’umma, wanda ya haifar da kiraye-kirayen daukar tsauraran matakai don hana afkuwar irin wannan a nan gaba. ‘Yan Nijeriya sun bibiyi sabbin bayanai game da taron, suna ba da tallafi ta hanyar gudummawa da hadin kai.

Manyan al’amuran siyasa 10 da suka Ja Hankulan ‘yan Nijeriya a 2024

Yayin da shekara ta 2024 ke karatowa, Nijeriya ta ga dimbin al’amuran siyasa da suka shafi yanayin kasar. Tun daga sauye-sauyen siyasa zuwa fuskar diflomasiyya, wadannan al’amura sun yi tasiri matuka ga al’ummar kasar.

A cikin wannan rahoto, Tribune Online ta bayyana manyan al’amuran siyasa 10 da suka samar da kanun labarai a shekarar 2024.

Amincewa da Sabon taken Nijeriya

A wani yunkuri na inganta hadin kan kasa da kuma sanin su, gwamnatin Nijeriya ta maido da taken kasar na asali mai suna “Nigeria, We Heil You,” da ake amfani da i daga 1960 zuwa 1978.

Karin mafi karancin albashi

Gwamnati ta kara mafi karancin albashi na kasa daga Naira 30,000 zuwa Naira 70,000 a matsayin martani ga tsadar rayuwa. Wannan shawarar ta biyo bayan tsawaita tattaunawa tsakanin kungiyoyin kwadago da jami’an gwamnati.

Lalacewar babbar tashar wutar lantarki

Lalacewar tashar wutar lantarki ta kasa ta nuna irin kalubalen da ake fuskanta a fannin samar da wutar lantarki a Nijeriya, wanda ke kawo cikas ga rayuwar yau da kullum ga miliyoyin ‘yan Nijeriya.

Zanga-zangar kuncin Rayuwa

Zanga-zangar dai ta varke a fadin kasar a cikin mawuyacin hali na tsadar rayuwa, lamarin da ‘yan Nijeriya suka dora alhakinsa kan sabbin sauye-sauyen da Shugaba Bola Tinubu ya yi. Akalla mutane 11 aka kashe, sannan an kama dan jarida daya.

Yi wa Majalisar ministoci kasa garanbawul

Shugaba Tinubu ya aiwatar da garambawul a majalisar ministocinsa, inda ya kori ministocin ilimi, yawon shakatawa, Harkokin mata, da ci gaban matasa, da karamar ministar gidaje.

Zaven Shugaban kasar Amurka

Zaven shugaban kasar Amurka na 2024 ya jawo hankulan ‘yan Nijeriya matuka, musamman saboda tasirin da manufofin ‘yan takara za su yi a Nijeriya.

Fashewar bam a Ibadan

Wani abu da ya fashe a garin Ibadan na Jihar Oyo, ya nuna raunin al’amuran tsaro da ka’idojin birane, wanda ya yi sanadin asarar rayuka da jikkata wasu.

Garkuwa da daliban Kuriga

An yi garkuwa da yara dalibai sama da 200 da wani malami a garin Kuriga, Kaduna, amma daga baya aka sako su.

Turmutsutsun Ibadan da Anambra da kuma Abuja

Turmutsutsun da ya afku a sassa daban-daban na kasar ya haifar da hasarar rayuka da jikkatar jama’a, lamarin da ke nuna bukatar inganta matakan dakile cunkoson jama’a da kuma tsarin bayar da agajin gaggawa.

Takaddama Tsakanin Shettima Da Badenoch

Rikicin a bainar jama’a tsakanin shugabar jam’iyyar Conservative ta Burtaniya Kemi Badenoch da mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima ya gwada karfin diflomasiyyar Nijeriya da dangantakarta da manyan abokan huldar kasa da kasa.

Matsalar Tsaro- bayyanar ‘yan ta’addar Lakurawa

Hukumomi da jama’a a Jihar Sakkwato da ke yankin arewa maso yammacin Nijeriya na nuna damuwa kan vullar wata kungiyar ta masu ikirarin jihadi da ke gudanar da

Hankali
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Kyawawan Dabi’un Annabi Muhammadu (SAW)

Kyawawan Dabi’un Annabi Muhammadu (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.