ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Dawo Da Zirga-zirgar Jiragen Sama A Filin Jirgin Sama Na Kaduna

by Sulaiman
2 years ago
Jirgin Sama

An dawo da zirga-zirgar jirage a filin jirgin sama na Hassan Usman Katsina, da ke Kaduna bayan da hukumomi suka dakatar da zirga-zirgar jiragen a Kaduna saboda rashin tsaro. Jirgin Air Peace ERJ-145, ya sauka a filin jirgin da misalin karfe 5:10 na yammacin ranar Litinin.

don sanar da sake dawo da zirga-zirgar jiragen sama a babban birnin jihar, tun bayan dakatar da zirga-zirgar jiragen a filin tashi da saukar jiragen a watan Maris din shekarar 2022, sakamakon harin da ‘yan bindiga suka kai musu. Fasinjoji da masu gudanar da harkokin kasuwanci a kusa da filin jirgin sun bayyana farin cikinsu da sake dawo wa da zirga-zirgar jiragen a filin jirgin amma sun yi kira ga hukumomin da abin ya shafa da su tura karin jami’an tsaro tare da tabbatar da tsaro a ciki da wajen filin jirgin.

  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Fashin Daji Da Dama, Sun Kwato Makamai A Sokoto
  • Me Ya Sa Dangantaka Da Sin Ke Samun Karbuwa A Afrika?

Shugaba mai kula da filin jirgin, Adamu Sheikh, ya ce, akwai sauran kamfanonin jiragen sama da za su fara zirga-zirga zuwa Kaduna, ya kuma ba da tabbacin cewa an samar da isasshen tsaro da kayan aiki don sauka da tashi a filin jirgin.

ADVERTISEMENT

Mai kula da jiragen Air Peace da ke Kaduna, Fatima Ndayako ta shaida wa manema labarai cewa, “kamfanin ya dawo da zirga-zirgarsa ne Kaduna saboda yawan kiraye-kiraye da abokan cinikinmu ke yi na bukatar dawo wa.” Ta ce, Air Peace zai rika gudanar da ayyukanshi na yau da kullum daga Kaduna zuwa Legas, ta kara da cewa “a halin yanzu. , Air Peace ne kawai jirgin da ke aiki tsakanin Legas da Kaduna a filin jirgin sama na Kaduna, inda ya samar da jiragen da za su dauki fasinjoji 50 kacal.”

An tattaro cewa, gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani ne ya taimaka wajen dawo da ayyukan jiragen sama a jihar bayan ganawa da shugabannin kamfanonin jiragen sama a Abuja tare da ba su tabbacin daukar matakan tsaro da suka dace.

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Fika

Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Fika Ya Rasu Yana Da Shekara 90

LABARAI MASU NASABA

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.