• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Fara Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa Da Na ‘Yan Majalisa A Turkiyya

by Muhammad
2 years ago
in Kasashen Ketare
0
An Fara Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa Da Na ‘Yan Majalisa A Turkiyya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau masu zabe daga fadin Turkiyya za su nufi rumfunan zabe domin kada kuri’a a zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisa.

An fara zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisa a fadin Turkiyya da safiyar Lahadi. Shugaban kasa mai ci Recep Tayyip Erdogan yana neman wani wa’adi sa’annan daga bangaren adawa Kemal Kilicdaroglu na Nation’s Alliance da kuma Sinan Ogan na Ata Alliance su ma suna takarar.

  • Yunkurin Masu Ruwa Da Tsaki A Nahiyar Afirka Wajen Samar Da Takin Zamani

Kafar yada labaran kasar TRT HAUS ta ce, Hukumar zaben Turkiyya mai zaman kanta YSK ta sanar da cewa sama da ‘yan kasar miliyan 64 ne suka cancanta su jefa kuri’a a zaben 14 ga watan Mayu, daga cikin har da masu zabe sama da miliyan uku da ke a kasar waje.

Za a kammala jefa kuri’a da misalin karfe 5:00 agogon Turkiyya, haka kuma ana sa ran sakamako farko zai soma shigowa ba da jimawa ba.

Ana bukatar masu zabe a Turkiyya su nuna katin shaidarsu na dan kasa da sauran katukan da ake bukata a rumfar zabe domin jefa kuri’a.

Labarai Masu Nasaba

Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah

Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan HulÉ—a

Daga nan ne ake ba mai zabe takardun jefa kuri’a biyu, daya ta shugaban kasa sai kuma daya ta ‘yan majalisa. Hukumar zaben kasar ta bayyana cewa ba a yarda masu zaben su dauki hoto ko bidiyo ba a wuraren zaben, kuma ana bukatar su bar wayoyinsu a waje.

Bayan an kammala zaben, kuri’un da aka jefa na shugaban kasa ana kirga su a gaban kwamitin zaben wanda ya kunshi jami’an hukumar zaben da kuma wakilan jam’iyyu da kuma jama’ar da suka yi zaben.

Duka ‘yan kasa za su iya zabe Hukumar zaben Turkiyya ta dauki matakai domin tabbatar da cewa ta sa zaben ya zo da sauki ga duka jama’ar kasar ko da suna da bukata ta musamman.

Ga wadanda ba za su iya barin gidajensu ko kuma gadon asibitinsu ba, akwai akwatunan zabe na tafi da gidanka da aka tanadar.

Za a kai wadannan akwatuna inda suke domin ganin cewa sun yi zabensu. Wata mafita kuma ita ce za a iya amfani da motar kwana-kwana ta asibiti domin kai marar lafiya jefa kuri’a a kyauta.

Haka kuma hukumar zaben ta tanadi takardun zabe na musamman ga masu larurar gani. Wadannan takardun suna da gwaragwaran rubutu da kuma haruffan makafi domin su iya zabe ba tare da an tallafa musu ba.

Duka wadannan tsare-tsaren an yi su ne domin tabbatar da cewa duka jama’ar kasar za su iya zabe cikin martaba. An kawo kuri’un ‘yan Turkiyya mazauna kasar waje ta jirgin sama kuma za a kirga su a lokacin daya da wadanda aka jefa a Turkiyya.

An soma jefa kuri’u a kasashen waje tsakanin 27 ga watan Afrilu aka kammala 9 ga watan Mayu.

A babban zaben, dole ne jam’iyya ta samu akalla kashi 10 na kuri’un da aka jefa a fadin kasar kafin dan takararta ya samu kujera a majalisa.

Jam’iyyun hadaka ne kawai za su wuce kashi goma ga jam’iyyunsu su samu kujera. A ranar zabe, an haramta wa duk wata kafar watsa labarai saka duk wata talla ta siyasa ko hasashe ko kuma sharhi kan siyasa har zuwa karfe 6:00 na yamma (1500GMT).

Tsakanin 06:00PM (1500GMT) da 9:00PM (1800GMT), kafafen watsa labarai za su iya wallafa sanarwa kan zabe wadda hukumar zabe ta bayar.

Haka kuma za a haramta sayar da barasa daga 6:00 na safe (0300GMT) zuwa 12:00 na dare (2100GMT), haka an haramta shan giya a bainar jama’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Recep Tayyip ErdoganZabeZaben Turkiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yunkurin Masu Ruwa Da Tsaki A Nahiyar Afirka Wajen Samar Da Takin Zamani

Next Post

Dakatar Da Shigo Da Manja: Kwararru A Nijeriya Sun Bukaci A Zuba Jari Mai Yawa A Fannin

Related

Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah

20 hours ago
Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan HulÉ—a
Kasashen Ketare

Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan HulÉ—a

2 days ago
Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini
Kasashen Ketare

Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini

3 days ago
Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon
Kasashen Ketare

Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon

6 days ago
Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
Ilimi

Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China

1 week ago
Gwamnatin Trump Na Shirin Rufe Ofisoshin Jakadanci A Afrika
Kasashen Ketare

Gwamnatin Trump Na Shirin Rufe Ofisoshin Jakadanci A Afrika

3 weeks ago
Next Post
Dakatar Da Shigo Da Manja: Kwararru A Nijeriya Sun Bukaci A Zuba Jari Mai Yawa A Fannin

Dakatar Da Shigo Da Manja: Kwararru A Nijeriya Sun Bukaci A Zuba Jari Mai Yawa A Fannin

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

May 8, 2025
An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.