ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Fara Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa Da Na ‘Yan Majalisa A Turkiyya

by Muhammad
3 years ago
Turkiyya

A yau masu zabe daga fadin Turkiyya za su nufi rumfunan zabe domin kada kuri’a a zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisa.

An fara zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisa a fadin Turkiyya da safiyar Lahadi. Shugaban kasa mai ci Recep Tayyip Erdogan yana neman wani wa’adi sa’annan daga bangaren adawa Kemal Kilicdaroglu na Nation’s Alliance da kuma Sinan Ogan na Ata Alliance su ma suna takarar.

  • Yunkurin Masu Ruwa Da Tsaki A Nahiyar Afirka Wajen Samar Da Takin Zamani

Kafar yada labaran kasar TRT HAUS ta ce, Hukumar zaben Turkiyya mai zaman kanta YSK ta sanar da cewa sama da ‘yan kasar miliyan 64 ne suka cancanta su jefa kuri’a a zaben 14 ga watan Mayu, daga cikin har da masu zabe sama da miliyan uku da ke a kasar waje.

ADVERTISEMENT

Za a kammala jefa kuri’a da misalin karfe 5:00 agogon Turkiyya, haka kuma ana sa ran sakamako farko zai soma shigowa ba da jimawa ba.

Ana bukatar masu zabe a Turkiyya su nuna katin shaidarsu na dan kasa da sauran katukan da ake bukata a rumfar zabe domin jefa kuri’a.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Daga nan ne ake ba mai zabe takardun jefa kuri’a biyu, daya ta shugaban kasa sai kuma daya ta ‘yan majalisa. Hukumar zaben kasar ta bayyana cewa ba a yarda masu zaben su dauki hoto ko bidiyo ba a wuraren zaben, kuma ana bukatar su bar wayoyinsu a waje.

Bayan an kammala zaben, kuri’un da aka jefa na shugaban kasa ana kirga su a gaban kwamitin zaben wanda ya kunshi jami’an hukumar zaben da kuma wakilan jam’iyyu da kuma jama’ar da suka yi zaben.

Duka ‘yan kasa za su iya zabe Hukumar zaben Turkiyya ta dauki matakai domin tabbatar da cewa ta sa zaben ya zo da sauki ga duka jama’ar kasar ko da suna da bukata ta musamman.

Ga wadanda ba za su iya barin gidajensu ko kuma gadon asibitinsu ba, akwai akwatunan zabe na tafi da gidanka da aka tanadar.

Za a kai wadannan akwatuna inda suke domin ganin cewa sun yi zabensu. Wata mafita kuma ita ce za a iya amfani da motar kwana-kwana ta asibiti domin kai marar lafiya jefa kuri’a a kyauta.

Haka kuma hukumar zaben ta tanadi takardun zabe na musamman ga masu larurar gani. Wadannan takardun suna da gwaragwaran rubutu da kuma haruffan makafi domin su iya zabe ba tare da an tallafa musu ba.

Duka wadannan tsare-tsaren an yi su ne domin tabbatar da cewa duka jama’ar kasar za su iya zabe cikin martaba. An kawo kuri’un ‘yan Turkiyya mazauna kasar waje ta jirgin sama kuma za a kirga su a lokacin daya da wadanda aka jefa a Turkiyya.

An soma jefa kuri’u a kasashen waje tsakanin 27 ga watan Afrilu aka kammala 9 ga watan Mayu.

A babban zaben, dole ne jam’iyya ta samu akalla kashi 10 na kuri’un da aka jefa a fadin kasar kafin dan takararta ya samu kujera a majalisa.

Jam’iyyun hadaka ne kawai za su wuce kashi goma ga jam’iyyunsu su samu kujera. A ranar zabe, an haramta wa duk wata kafar watsa labarai saka duk wata talla ta siyasa ko hasashe ko kuma sharhi kan siyasa har zuwa karfe 6:00 na yamma (1500GMT).

Tsakanin 06:00PM (1500GMT) da 9:00PM (1800GMT), kafafen watsa labarai za su iya wallafa sanarwa kan zabe wadda hukumar zabe ta bayar.

Haka kuma za a haramta sayar da barasa daga 6:00 na safe (0300GMT) zuwa 12:00 na dare (2100GMT), haka an haramta shan giya a bainar jama’a.

Turkiyya
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
  • Muhammad
    ‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Kasashen Ketare

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
Kasashen Ketare

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

July 5, 2026
Next Post
Dakatar Da Shigo Da Manja: Kwararru A Nijeriya Sun Bukaci A Zuba Jari Mai Yawa A Fannin

Dakatar Da Shigo Da Manja: Kwararru A Nijeriya Sun Bukaci A Zuba Jari Mai Yawa A Fannin

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.