ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Fara Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa Da Na ‘Yan Majalisa A Turkiyya

by Muhammad
3 years ago
Turkiyya

A yau masu zabe daga fadin Turkiyya za su nufi rumfunan zabe domin kada kuri’a a zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisa.

An fara zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisa a fadin Turkiyya da safiyar Lahadi. Shugaban kasa mai ci Recep Tayyip Erdogan yana neman wani wa’adi sa’annan daga bangaren adawa Kemal Kilicdaroglu na Nation’s Alliance da kuma Sinan Ogan na Ata Alliance su ma suna takarar.

  • Yunkurin Masu Ruwa Da Tsaki A Nahiyar Afirka Wajen Samar Da Takin Zamani

Kafar yada labaran kasar TRT HAUS ta ce, Hukumar zaben Turkiyya mai zaman kanta YSK ta sanar da cewa sama da ‘yan kasar miliyan 64 ne suka cancanta su jefa kuri’a a zaben 14 ga watan Mayu, daga cikin har da masu zabe sama da miliyan uku da ke a kasar waje.

ADVERTISEMENT

Za a kammala jefa kuri’a da misalin karfe 5:00 agogon Turkiyya, haka kuma ana sa ran sakamako farko zai soma shigowa ba da jimawa ba.

Ana bukatar masu zabe a Turkiyya su nuna katin shaidarsu na dan kasa da sauran katukan da ake bukata a rumfar zabe domin jefa kuri’a.

LABARAI MASU NASABA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

Daga nan ne ake ba mai zabe takardun jefa kuri’a biyu, daya ta shugaban kasa sai kuma daya ta ‘yan majalisa. Hukumar zaben kasar ta bayyana cewa ba a yarda masu zaben su dauki hoto ko bidiyo ba a wuraren zaben, kuma ana bukatar su bar wayoyinsu a waje.

Bayan an kammala zaben, kuri’un da aka jefa na shugaban kasa ana kirga su a gaban kwamitin zaben wanda ya kunshi jami’an hukumar zaben da kuma wakilan jam’iyyu da kuma jama’ar da suka yi zaben.

Duka ‘yan kasa za su iya zabe Hukumar zaben Turkiyya ta dauki matakai domin tabbatar da cewa ta sa zaben ya zo da sauki ga duka jama’ar kasar ko da suna da bukata ta musamman.

Ga wadanda ba za su iya barin gidajensu ko kuma gadon asibitinsu ba, akwai akwatunan zabe na tafi da gidanka da aka tanadar.

Za a kai wadannan akwatuna inda suke domin ganin cewa sun yi zabensu. Wata mafita kuma ita ce za a iya amfani da motar kwana-kwana ta asibiti domin kai marar lafiya jefa kuri’a a kyauta.

Haka kuma hukumar zaben ta tanadi takardun zabe na musamman ga masu larurar gani. Wadannan takardun suna da gwaragwaran rubutu da kuma haruffan makafi domin su iya zabe ba tare da an tallafa musu ba.

Duka wadannan tsare-tsaren an yi su ne domin tabbatar da cewa duka jama’ar kasar za su iya zabe cikin martaba. An kawo kuri’un ‘yan Turkiyya mazauna kasar waje ta jirgin sama kuma za a kirga su a lokacin daya da wadanda aka jefa a Turkiyya.

An soma jefa kuri’u a kasashen waje tsakanin 27 ga watan Afrilu aka kammala 9 ga watan Mayu.

A babban zaben, dole ne jam’iyya ta samu akalla kashi 10 na kuri’un da aka jefa a fadin kasar kafin dan takararta ya samu kujera a majalisa.

Jam’iyyun hadaka ne kawai za su wuce kashi goma ga jam’iyyunsu su samu kujera. A ranar zabe, an haramta wa duk wata kafar watsa labarai saka duk wata talla ta siyasa ko hasashe ko kuma sharhi kan siyasa har zuwa karfe 6:00 na yamma (1500GMT).

Tsakanin 06:00PM (1500GMT) da 9:00PM (1800GMT), kafafen watsa labarai za su iya wallafa sanarwa kan zabe wadda hukumar zabe ta bayar.

Haka kuma za a haramta sayar da barasa daga 6:00 na safe (0300GMT) zuwa 12:00 na dare (2100GMT), haka an haramta shan giya a bainar jama’a.

Turkiyya
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya
Kasashen Ketare

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

June 23, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Kasashen Ketare

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

June 22, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran
Kasashen Ketare

Iran Ta Ce Shirinta Na Makamai Masu Linzami Ba Ya Cikin Tattaunawa Da Amurka

June 18, 2026
Next Post
Dakatar Da Shigo Da Manja: Kwararru A Nijeriya Sun Bukaci A Zuba Jari Mai Yawa A Fannin

Dakatar Da Shigo Da Manja: Kwararru A Nijeriya Sun Bukaci A Zuba Jari Mai Yawa A Fannin

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.