ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yunkurin Masu Ruwa Da Tsaki A Nahiyar Afirka Wajen Samar Da Takin Zamani

by Abubakar Abba
3 years ago
Takin Zamani

Daya daga cikin abinda ke ciwa fannin aikin noma Tuwo a Kwarya a nahiyar Afirka shine karancin takin zamani.

Sai dai, domin a lalubo da mafita kan wannan kalubalen, wasu hukumomi sun dukufa kan yadda za su manoma a nahiyar sun samar wa da manoma takin, musamman kan farashi mai sauki.

  • An Jefar Da Jariri Dan Kwana 2 A Sansanin ‘Yan Gundun Hijira A Edo
  • Sudan: Jami’o’in Nijeriya Sun Sha Alwashin Bai Wa Daliban Da Aka Kwaso Guraben Karatu

Misali, hukumar samar da abinci da kuma bunkasa aikin noma da ke a karkashin majalisar dinkin duniya FAO da kuma shirin samar da abinci da ke a  karkashin majalisar WFP sun yi hasashen cewa, za a samu karancin abinci saboda tarnakin da fannin na samar da abinci ke fuskanta.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, don a magance irin wannan kalubalen, masu ruwa da tsaki a fadin duniya a fannin aikin noma sun gudanar da taro, inda suka yi nuni da cewa, akwai matukar bukatar a yi amfani da kayan aikin noma na zamani, musamman don a tabbatar kananan manoma sun samu takin zamani kuma kan lokaci don a samar da abinci, musamman mai gina jiki ga alumma.

Wasu daga cikin tattaunawar da aka yi irin wannan tarukan, sun nuna yadda wasu yankunan da ke a nahiyar Afirka ke kan yin kokari wajen samar da wadatacen takin zamani da ilimantar da manoman kan sanin ingantacciyar kasar noma da za su yi shuka akai da yadda za su zuba takin zamani da sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Har ila yau masu bayar da dauki a fannin aikin noma sun zuba dala biliyan 30,musamman don a bunkasa yin noma a nahiyar Afirka ke na sama da shekaru hudu  masu zuwa.

Baya ga wannan, mahalarta taron sun kuma yi kira da a gaggauta samar da takin zamani ga manoman da ke a nahiyar kuma a cikin farashi mai sauki.

A cewar kungiyar masana’antun sarrafa takin zamani ta kasa da kasa, a nahiyar Afirka IFA, ana yin amfani da buhun takin zamani mai nauyin kilo 12 a kowacce kadadar noma daya.

Hakazalika, Cibiyar bincike kan tsare -tsaren abinci ta kasa da kasa IFPRI ta bayyana cewa, takin zamani da moma ke yin amfani da shi a Nijeriya da Kenya da kuma wasu sassan a Afrika ako wacca kadadar yin noma, ya kai kasa da kilo 50 idan aka yi la’akari da yadda ake yin amfani da shi Malaysiya, inda ake yin amfani da akalla kilo 1,570 ako wacce kadadar noma daya sai kuma a kasar Hong Kong, inda ake yin amfani da kilo 1,297 ako wacce kadadar noma daya, inda kuma a kasar Bangladesh ake yin amfani da akalla kilo 278 ako wacce kadadar noma daya.

Bugu da kari, Cibiyoyi ta IFPRI ita ma ta goyi bayan taron musamman don tattauna wa kan yadda za a samar wa da manoma da ke a nahiyar  takin zamani da kuma samar wa masu safarar takin kudade  don a shigo da sanadaran da ake sarrafa takin zamanin.

Hakazalika, kulab din da ke samar wa da manoma takin zamani wato Afrikom, shi ma ya gudanar da wata ganawa a Accra, babban birinin kasar Ghana kan yadda za a samar wa da manoma takin zamani.

Kulab din ya gudanar da ganawar ce wadda ta kasance a karon farko bisa hadaka da Cibiyar habaka takin zamani ta kasa da kasa IFDC tare da kuma kungiyar samar da takin zamani a  yammacin Afrika WAFA.

Sun yi hakan ne bisa kokarin yadda za a samar wa da manoma takin zamani a Afrika da kuma irin sauye -sauyen da aka samu a fannin na samar da takin zamani a Afrika.

Takin Zamani
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
An Fara Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa Da Na ‘Yan Majalisa A Turkiyya

An Fara Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa Da Na 'Yan Majalisa A Turkiyya

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.