ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yunkurin Masu Ruwa Da Tsaki A Nahiyar Afirka Wajen Samar Da Takin Zamani

by Abubakar Abba
3 years ago
Takin Zamani

Daya daga cikin abinda ke ciwa fannin aikin noma Tuwo a Kwarya a nahiyar Afirka shine karancin takin zamani.

Sai dai, domin a lalubo da mafita kan wannan kalubalen, wasu hukumomi sun dukufa kan yadda za su manoma a nahiyar sun samar wa da manoma takin, musamman kan farashi mai sauki.

  • An Jefar Da Jariri Dan Kwana 2 A Sansanin ‘Yan Gundun Hijira A Edo
  • Sudan: Jami’o’in Nijeriya Sun Sha Alwashin Bai Wa Daliban Da Aka Kwaso Guraben Karatu

Misali, hukumar samar da abinci da kuma bunkasa aikin noma da ke a karkashin majalisar dinkin duniya FAO da kuma shirin samar da abinci da ke a  karkashin majalisar WFP sun yi hasashen cewa, za a samu karancin abinci saboda tarnakin da fannin na samar da abinci ke fuskanta.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, don a magance irin wannan kalubalen, masu ruwa da tsaki a fadin duniya a fannin aikin noma sun gudanar da taro, inda suka yi nuni da cewa, akwai matukar bukatar a yi amfani da kayan aikin noma na zamani, musamman don a tabbatar kananan manoma sun samu takin zamani kuma kan lokaci don a samar da abinci, musamman mai gina jiki ga alumma.

Wasu daga cikin tattaunawar da aka yi irin wannan tarukan, sun nuna yadda wasu yankunan da ke a nahiyar Afirka ke kan yin kokari wajen samar da wadatacen takin zamani da ilimantar da manoman kan sanin ingantacciyar kasar noma da za su yi shuka akai da yadda za su zuba takin zamani da sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Har ila yau masu bayar da dauki a fannin aikin noma sun zuba dala biliyan 30,musamman don a bunkasa yin noma a nahiyar Afirka ke na sama da shekaru hudu  masu zuwa.

Baya ga wannan, mahalarta taron sun kuma yi kira da a gaggauta samar da takin zamani ga manoman da ke a nahiyar kuma a cikin farashi mai sauki.

A cewar kungiyar masana’antun sarrafa takin zamani ta kasa da kasa, a nahiyar Afirka IFA, ana yin amfani da buhun takin zamani mai nauyin kilo 12 a kowacce kadadar noma daya.

Hakazalika, Cibiyar bincike kan tsare -tsaren abinci ta kasa da kasa IFPRI ta bayyana cewa, takin zamani da moma ke yin amfani da shi a Nijeriya da Kenya da kuma wasu sassan a Afrika ako wacca kadadar yin noma, ya kai kasa da kilo 50 idan aka yi la’akari da yadda ake yin amfani da shi Malaysiya, inda ake yin amfani da akalla kilo 1,570 ako wacce kadadar noma daya sai kuma a kasar Hong Kong, inda ake yin amfani da kilo 1,297 ako wacce kadadar noma daya, inda kuma a kasar Bangladesh ake yin amfani da akalla kilo 278 ako wacce kadadar noma daya.

Bugu da kari, Cibiyoyi ta IFPRI ita ma ta goyi bayan taron musamman don tattauna wa kan yadda za a samar wa da manoma da ke a nahiyar  takin zamani da kuma samar wa masu safarar takin kudade  don a shigo da sanadaran da ake sarrafa takin zamanin.

Hakazalika, kulab din da ke samar wa da manoma takin zamani wato Afrikom, shi ma ya gudanar da wata ganawa a Accra, babban birinin kasar Ghana kan yadda za a samar wa da manoma takin zamani.

Kulab din ya gudanar da ganawar ce wadda ta kasance a karon farko bisa hadaka da Cibiyar habaka takin zamani ta kasa da kasa IFDC tare da kuma kungiyar samar da takin zamani a  yammacin Afrika WAFA.

Sun yi hakan ne bisa kokarin yadda za a samar wa da manoma takin zamani a Afrika da kuma irin sauye -sauyen da aka samu a fannin na samar da takin zamani a Afrika.

Takin Zamani
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
An Fara Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa Da Na ‘Yan Majalisa A Turkiyya

An Fara Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa Da Na 'Yan Majalisa A Turkiyya

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Takin Zamani

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Takin Zamani

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.