• English
  • Business News
Friday, September 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gano Cututtuka Uku Da Suka Ta Da Hankalin Hukumomin Lafiya A Nijeriya

by Rabi'u Ali Indabawa
2 hours ago
in Labarai
0
An Gano Cututtuka Uku Da Suka Ta Da Hankalin Hukumomin Lafiya A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akalla jihohi biyu tare da babban birnin Nijeriya, Abuja ne suka fuskanci barkewar wasu cutuka a makon da ya gabata da wanda ake ciki, al’amarin da ya tayar da hankalin al’umma da hukumomi.

Adamawa

An samu barkewar wata bakuwar cuta mai zagwanye naman jikin mutum da ta yi sanadiyyar mutuwar mutum bakwai.

  • Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace
  • An Shirya Bikin Kaddamar Da Shirin Gaskiya Na Talabijin “Laszlo Hudec” Cikin Harshen Slovak A Kasar Slovakia

Kaduna

Ita ma ta samu barkewar cutar da hukumomi suka ce Mashako ce wadda ta kashe yara biyu sannan ta tilasta rufe makarantun jihar.

Labarai Masu Nasaba

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina: Nasara Ko Matsala?

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Bincike A Kan Fashewar Wani Abu A Kaduna

Ita kuwa Abuja Babban Birnin Nijeriya ta samu wasu marasa lafiya guda biyu da wani nau’in zazzabi da ke sa mutane zubar da jini amma hukumomi sun ce ba a sami marasa lafiyar da Lassa ko kuma Ebola ba.

Cuta mai zagwanye naman jikin dan’adam

Kamfanin dillancin labarai na Nijeriya, NAN ya rawaito cewa cutar da ta yi sanadiyyar mutuwar mutum bakwai a Jihar Adamawa tana faraway ne daga kuraje.

Daga nan kuma sai su fashe tare da zagwanyewa inda wani lokacin ma suke side fatar har su tarar da kashi a gabar da cutar ta shafa.

Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO ta bayyana cutar kuraje ta Buruli Ulcer da daya daga cikin cutukan da ba a fiya mayar da kai a kansu ba a duniya.

WHO ta kuma ce cutar na barkewa a karkara musamman da ke kusa da ruwa da ke fama da rashin asibitoci.

Jami’i a shirin kasa na dakile cutar tarin fuka da kuturta a Nijeriya, Dr Adesigbin Olufemi ya sanar da cewa an samu masu dauke da cutar su 67, inda za a yi wa mutum 8 tiyata.

Olufemi wanda ya bayyana hakan a ranar Lahadi ya ce duk da cewa ba a gano dalilin faruwar cutar ba amma an fi zaton cewa cutar kuraje ce ta Buruli Ulcer wadda ake ci gaba da binciken gano bayanai a kanta.

Zazzabi da aman jini a Abuja

Babban Birnin Tarayyar Nijeriya, Abuja ya fuskanci wata bakuwar cuta a karshen makon da ya gabata, al’amarin da ya jefa al’ummar birnin cikin razani da fargaba.

Bayanai dai sun nuna cewa an samu wasu mutum biyu da zazzabi mai tsanani tare da aman jini ta baki da hanci da ta dubura a wani asibiti da ke birnin.

Bayanai sun nuna cewa daya daga cikin mutanen ya yi bulaguro zuwa kasar Rwanda domin yawan bude idanu, inda kuma tun a Rwandar ya fara fuskantar alamun cutar.

Ba tare da bata lokaci ba sai asibitin ya sanar da hukumar da ke dakile cutuka masu yaduwa ta Nijeriya, NCDC wadda kuma ta umarci jami’anta su yi gwaje-gwaje domin gano ko cutar na da alaka da zazzabin cutar Ebola da Marburg da Dengue da kuma na Lassa.

Tuni hukumomi ciki har da hukumar dakile cutuka masu yaduwa ta Kano ta gargadi al’ummar jihar da su kula da shigi da ficin al’umma kasancewar jihar na da tarihin shigi da fici kasancewarta cibiyar kasuwanci.

Mashako a Kaduna

Sakamakon barkewar cutar ta mashako da ta yi sanadiyyar mutuwar yara guda biyu Karamar Hukumar Birnin Gwari da ke Kaduna, hukumomi sun rufe makarantu a yankin na tsawon mako guda.

Kwamishiniyar lafiya a jihar Dr. Umma Kulthum Ahmed ta ce an rufe makarantun ne saboda kauce wa karuwar yaduwar cutar a tsakanin dalibai, ganin cewar yara kanan ne suka fi kamuwa da cutar.

Fiye da mutum 40 aka killace da suka kamu da cutar sai dai daga bisani an sallami wasu da dama daga cikinsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cututtuka
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Bayar Da Sabuwar Gudummawa Dangane Da Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya

Next Post

Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka’idojin Kasuwa

Related

Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda
Labarai

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina: Nasara Ko Matsala?

1 hour ago
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru
Labarai

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Bincike A Kan Fashewar Wani Abu A Kaduna

5 hours ago
Trump Ya Haramta Wa Jami’an Nijeriya Masu Cin Hanci Da Rashawa Shiga Amurka
Labarai

Trump Ya Haramta Wa Jami’an Nijeriya Masu Cin Hanci Da Rashawa Shiga Amurka

6 hours ago
NECO 2025: Gwamnan Kano Ya Bayyana Bayanai Ba Daidai Ba
Manyan Labarai

NECO 2025: Gwamnan Kano Ya Bayyana Bayanai Ba Daidai Ba

11 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Mika Ƙorafe-Ƙorafe Kan Sheikh Lawan Triumph Zuwa Majalisar Shura
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Mika Ƙorafe-Ƙorafe Kan Sheikh Lawan Triumph Zuwa Majalisar Shura

13 hours ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Yadda Gwamnoni Suke Kawo Cikas
Manyan Labarai

‘Yancin Kananan Hukumomi: Yadda Gwamnoni Suke Kawo Cikas

13 hours ago
Next Post
Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka’idojin Kasuwa

Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka'idojin Kasuwa

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

September 26, 2025
A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

September 26, 2025
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina: Nasara Ko Matsala?

September 26, 2025
Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka’idojin Kasuwa

Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka’idojin Kasuwa

September 26, 2025
An Gano Cututtuka Uku Da Suka Ta Da Hankalin Hukumomin Lafiya A Nijeriya

An Gano Cututtuka Uku Da Suka Ta Da Hankalin Hukumomin Lafiya A Nijeriya

September 26, 2025
Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Bayar Da Sabuwar Gudummawa Dangane Da Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya

Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Bayar Da Sabuwar Gudummawa Dangane Da Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya

September 26, 2025
Membobin Tawagar Koli Ta Sin Sun Ziyarci Jami’ai Da Gidajen Al’umma A Yankunan Jihar Xinjiang

Membobin Tawagar Koli Ta Sin Sun Ziyarci Jami’ai Da Gidajen Al’umma A Yankunan Jihar Xinjiang

September 26, 2025
Akwai Bukatar Sin Da Amurka Su Lalubo Hanya Mafi Dacewa Ta Tafiya Tare A Sabon Zamani

Akwai Bukatar Sin Da Amurka Su Lalubo Hanya Mafi Dacewa Ta Tafiya Tare A Sabon Zamani

September 26, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Bincike A Kan Fashewar Wani Abu A Kaduna

September 26, 2025
An Samu Manyan Sauye-Sauye Na Zamani A Jihar Xinjiang Cikin Shekaru 70

An Samu Manyan Sauye-Sauye Na Zamani A Jihar Xinjiang Cikin Shekaru 70

September 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.