ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gano Cututtuka Uku Da Suka Ta Da Hankalin Hukumomin Lafiya A Nijeriya

by Rabi'u Ali Indabawa
9 months ago
Cututtuka

Akalla jihohi biyu tare da babban birnin Nijeriya, Abuja ne suka fuskanci barkewar wasu cutuka a makon da ya gabata da wanda ake ciki, al’amarin da ya tayar da hankalin al’umma da hukumomi.

Adamawa

An samu barkewar wata bakuwar cuta mai zagwanye naman jikin mutum da ta yi sanadiyyar mutuwar mutum bakwai.

ADVERTISEMENT
  • Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace
  • An Shirya Bikin Kaddamar Da Shirin Gaskiya Na Talabijin “Laszlo Hudec” Cikin Harshen Slovak A Kasar Slovakia

Kaduna

Ita ma ta samu barkewar cutar da hukumomi suka ce Mashako ce wadda ta kashe yara biyu sannan ta tilasta rufe makarantun jihar.

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Ita kuwa Abuja Babban Birnin Nijeriya ta samu wasu marasa lafiya guda biyu da wani nau’in zazzabi da ke sa mutane zubar da jini amma hukumomi sun ce ba a sami marasa lafiyar da Lassa ko kuma Ebola ba.

Cuta mai zagwanye naman jikin dan’adam

Kamfanin dillancin labarai na Nijeriya, NAN ya rawaito cewa cutar da ta yi sanadiyyar mutuwar mutum bakwai a Jihar Adamawa tana faraway ne daga kuraje.

Daga nan kuma sai su fashe tare da zagwanyewa inda wani lokacin ma suke side fatar har su tarar da kashi a gabar da cutar ta shafa.

Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO ta bayyana cutar kuraje ta Buruli Ulcer da daya daga cikin cutukan da ba a fiya mayar da kai a kansu ba a duniya.

WHO ta kuma ce cutar na barkewa a karkara musamman da ke kusa da ruwa da ke fama da rashin asibitoci.

Jami’i a shirin kasa na dakile cutar tarin fuka da kuturta a Nijeriya, Dr Adesigbin Olufemi ya sanar da cewa an samu masu dauke da cutar su 67, inda za a yi wa mutum 8 tiyata.

Olufemi wanda ya bayyana hakan a ranar Lahadi ya ce duk da cewa ba a gano dalilin faruwar cutar ba amma an fi zaton cewa cutar kuraje ce ta Buruli Ulcer wadda ake ci gaba da binciken gano bayanai a kanta.

Zazzabi da aman jini a Abuja

Babban Birnin Tarayyar Nijeriya, Abuja ya fuskanci wata bakuwar cuta a karshen makon da ya gabata, al’amarin da ya jefa al’ummar birnin cikin razani da fargaba.

Bayanai dai sun nuna cewa an samu wasu mutum biyu da zazzabi mai tsanani tare da aman jini ta baki da hanci da ta dubura a wani asibiti da ke birnin.

Bayanai sun nuna cewa daya daga cikin mutanen ya yi bulaguro zuwa kasar Rwanda domin yawan bude idanu, inda kuma tun a Rwandar ya fara fuskantar alamun cutar.

Ba tare da bata lokaci ba sai asibitin ya sanar da hukumar da ke dakile cutuka masu yaduwa ta Nijeriya, NCDC wadda kuma ta umarci jami’anta su yi gwaje-gwaje domin gano ko cutar na da alaka da zazzabin cutar Ebola da Marburg da Dengue da kuma na Lassa.

Tuni hukumomi ciki har da hukumar dakile cutuka masu yaduwa ta Kano ta gargadi al’ummar jihar da su kula da shigi da ficin al’umma kasancewar jihar na da tarihin shigi da fici kasancewarta cibiyar kasuwanci.

Mashako a Kaduna

Sakamakon barkewar cutar ta mashako da ta yi sanadiyyar mutuwar yara guda biyu Karamar Hukumar Birnin Gwari da ke Kaduna, hukumomi sun rufe makarantu a yankin na tsawon mako guda.

Kwamishiniyar lafiya a jihar Dr. Umma Kulthum Ahmed ta ce an rufe makarantun ne saboda kauce wa karuwar yaduwar cutar a tsakanin dalibai, ganin cewar yara kanan ne suka fi kamuwa da cutar.

Fiye da mutum 40 aka killace da suka kamu da cutar sai dai daga bisani an sallami wasu da dama daga cikinsu.

Cututtuka
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Next Post
Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka’idojin Kasuwa

Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka'idojin Kasuwa

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.