• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gurfanar Da Tsohon Mataimakin Kakakin Majalisar Ogun Kan Zargin Tada Zaune-Tsaye

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
An Gurfanar Da Tsohon Mataimakin Kakakin Majalisar Ogun Kan Zargin Tada Zaune-Tsaye
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An gurfanar da tsohon mataimakin kakakin majalisar dokokin Jihar Ogun, Oludare Kadiri a gaban wata kotun majistare da ke Abeokuta bisa zargin barazana ga rayuwa da kuma tada zaune-tsaye.

Hakan dai ya biyo bayan wani sabani da aka samu yi a ranar Talata a zauren majalisar yayin da Kadiri ya toshe babbar kofar shiga harabar majalisar.

  • Kwana 5 Ga Rantsuwa: Waiwaye Kan Rawar Da Matan Shugabannin Kasa Suka Taka A Baya
  • Tony Blair Ya Ziyarci Tinubu A Abuja

An kama Kadiri, mai shekaru 54, daga baya kuma aka tuhume shi da laifuka biyu na barazana ga rayuwa da kuma haddasa rashin zaman lafiya.

Sai dai ya ki amsa laifin da ake tuhumarsa da shi.

Watanni uku da suka gabata shi da magoya bayansa sun mamaye Majalisar don “tabbatar da” hukuncin soke dakatarwar da majalisar ta yi masa.

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

A watan Satumba, 2022 ne majalisar ta dakatar da dan majalisar da wani mutum bisa zargin tauye hakki na majalisar dokokin jihar.

An kuma tsige Kadiri a matsayin mataimakin kakakin majalisar.

Sai dai wata babbar kotun Jihar Ogun da ta zauna a Abeokuta a watan Maris ta soke dakatarwar da aka yi wa Kadiri tare da sauran.

A ranar Talatar da ta gabata ne aka yi zargin cewa ya rufe babbar kofar harabar majalisar inda ya dage cewa dole ne a bar shi ya ci gaba da zama dan majalisar dokokin jihar domin ya ci gaba da gudanar da aikinsa kamar yadda kotu ta umarce shi.

An ga jami’an tsaro suna lallashin dan majalisar tare da shiga tsakani.

An dai ga tsohon mataimakin kakakin ne zaune a cikin motarsa yana latsa wayarsa, yayin da lamarin ya ci tura.

Dan sanda mai gabatar da kara, Lawrence Olu-Balogun, ya shaida wa kotun cewa wanda ake kara ya aikata laifin ne a ranar 25 ga watan Maris da misalin karfe 8:40 na safe a harabar majalisar da ke Oke-Mosan.

Olu-Balogun ya ce wanda ake kara ya shiga harabar majalisar inda ya yi barazana ga rayuwar ‘yan majalisar da sauran jami’an da ke ciki.

Ya kuma kara da cewa wanda ake tuhumar ya kuma yi amfani da motarsa wajen tare kofar shiga majalisar.

Lauyan mai shigar da karar ya ce tsohon dan majalisar ya gudanar da kansa ne ta hanyar da za ta iya haifar da kawo matsala ga zaman lafiya ta hanyar kai hari wanda ya kawo cikas ga tsarin samar da doka a majalisar.

Olu-Balogun ya bayyana cewa an dakatar da wanda ake tuhuma tun watan Maris din 2022, amma ya yi ikirarin cewa ya samu hukunci daga wata babbar kotu a Ogun, inda ya nemi ya koma ofishinsa.

Ya kara da cewa a lokacin da wanda ake kara ya isa zauren majalisar, jami’an tsaron da ke kofar majalisar sun hana shi shiga harabar.

A cewar masa, laifukan sun ci karo da sashe na 86(1) da 249(D) na kundin laifuffuka na Ogun na shekarar 2006.

Babban alkalin kotun, Misis M.O. Osinbajo, ta ba da belinsa.

Alkalin kotun ta dage ci gaba da sauraren karar har zuwa ranar 1 ga watan Yuni.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KotuMajalisar DokokiogunTsohon Mataimakin Kakaki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwana 4 Ga Rantsuwa: Yadda Shugabannin Duniya Ke Tururuwar Rantsar Da Tinubu

Next Post

Za Mu Yi Nazarin Rahoton Mika Mulki Da Ganduje Ya Ba Mu -NNPP

Related

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

3 hours ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

5 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

8 hours ago
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato
Manyan Labarai

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

9 hours ago
Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa
Labarai

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

10 hours ago
DSS
Labarai

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

12 hours ago
Next Post
Za Mu Yi Nazarin Rahoton Mika Mulki Da Ganduje Ya Ba Mu -NNPP

Za Mu Yi Nazarin Rahoton Mika Mulki Da Ganduje Ya Ba Mu -NNPP

LABARAI MASU NASABA

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

June 4, 2025
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

June 4, 2025
Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

June 4, 2025
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

June 4, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

June 4, 2025
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

June 4, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.