ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gurfanar Da Tsohon Mataimakin Kakakin Majalisar Ogun Kan Zargin Tada Zaune-Tsaye

by Sadiq
3 years ago
Ogun

An gurfanar da tsohon mataimakin kakakin majalisar dokokin Jihar Ogun, Oludare Kadiri a gaban wata kotun majistare da ke Abeokuta bisa zargin barazana ga rayuwa da kuma tada zaune-tsaye.

Hakan dai ya biyo bayan wani sabani da aka samu yi a ranar Talata a zauren majalisar yayin da Kadiri ya toshe babbar kofar shiga harabar majalisar.

  • Kwana 5 Ga Rantsuwa: Waiwaye Kan Rawar Da Matan Shugabannin Kasa Suka Taka A Baya
  • Tony Blair Ya Ziyarci Tinubu A Abuja

An kama Kadiri, mai shekaru 54, daga baya kuma aka tuhume shi da laifuka biyu na barazana ga rayuwa da kuma haddasa rashin zaman lafiya.

ADVERTISEMENT

Sai dai ya ki amsa laifin da ake tuhumarsa da shi.

Watanni uku da suka gabata shi da magoya bayansa sun mamaye Majalisar don “tabbatar da” hukuncin soke dakatarwar da majalisar ta yi masa.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

A watan Satumba, 2022 ne majalisar ta dakatar da dan majalisar da wani mutum bisa zargin tauye hakki na majalisar dokokin jihar.

An kuma tsige Kadiri a matsayin mataimakin kakakin majalisar.

Sai dai wata babbar kotun Jihar Ogun da ta zauna a Abeokuta a watan Maris ta soke dakatarwar da aka yi wa Kadiri tare da sauran.

A ranar Talatar da ta gabata ne aka yi zargin cewa ya rufe babbar kofar harabar majalisar inda ya dage cewa dole ne a bar shi ya ci gaba da zama dan majalisar dokokin jihar domin ya ci gaba da gudanar da aikinsa kamar yadda kotu ta umarce shi.

An ga jami’an tsaro suna lallashin dan majalisar tare da shiga tsakani.

An dai ga tsohon mataimakin kakakin ne zaune a cikin motarsa yana latsa wayarsa, yayin da lamarin ya ci tura.

Dan sanda mai gabatar da kara, Lawrence Olu-Balogun, ya shaida wa kotun cewa wanda ake kara ya aikata laifin ne a ranar 25 ga watan Maris da misalin karfe 8:40 na safe a harabar majalisar da ke Oke-Mosan.

Olu-Balogun ya ce wanda ake kara ya shiga harabar majalisar inda ya yi barazana ga rayuwar ‘yan majalisar da sauran jami’an da ke ciki.

Ya kuma kara da cewa wanda ake tuhumar ya kuma yi amfani da motarsa wajen tare kofar shiga majalisar.

Lauyan mai shigar da karar ya ce tsohon dan majalisar ya gudanar da kansa ne ta hanyar da za ta iya haifar da kawo matsala ga zaman lafiya ta hanyar kai hari wanda ya kawo cikas ga tsarin samar da doka a majalisar.

Olu-Balogun ya bayyana cewa an dakatar da wanda ake tuhuma tun watan Maris din 2022, amma ya yi ikirarin cewa ya samu hukunci daga wata babbar kotu a Ogun, inda ya nemi ya koma ofishinsa.

Ya kara da cewa a lokacin da wanda ake kara ya isa zauren majalisar, jami’an tsaron da ke kofar majalisar sun hana shi shiga harabar.

A cewar masa, laifukan sun ci karo da sashe na 86(1) da 249(D) na kundin laifuffuka na Ogun na shekarar 2006.

Babban alkalin kotun, Misis M.O. Osinbajo, ta ba da belinsa.

Alkalin kotun ta dage ci gaba da sauraren karar har zuwa ranar 1 ga watan Yuni.

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Za Mu Yi Nazarin Rahoton Mika Mulki Da Ganduje Ya Ba Mu -NNPP

Za Mu Yi Nazarin Rahoton Mika Mulki Da Ganduje Ya Ba Mu -NNPP

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.