ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gurfanar Da Tsohon Mataimakin Kakakin Majalisar Ogun Kan Zargin Tada Zaune-Tsaye

by Sadiq
3 years ago
Ogun

An gurfanar da tsohon mataimakin kakakin majalisar dokokin Jihar Ogun, Oludare Kadiri a gaban wata kotun majistare da ke Abeokuta bisa zargin barazana ga rayuwa da kuma tada zaune-tsaye.

Hakan dai ya biyo bayan wani sabani da aka samu yi a ranar Talata a zauren majalisar yayin da Kadiri ya toshe babbar kofar shiga harabar majalisar.

  • Kwana 5 Ga Rantsuwa: Waiwaye Kan Rawar Da Matan Shugabannin Kasa Suka Taka A Baya
  • Tony Blair Ya Ziyarci Tinubu A Abuja

An kama Kadiri, mai shekaru 54, daga baya kuma aka tuhume shi da laifuka biyu na barazana ga rayuwa da kuma haddasa rashin zaman lafiya.

ADVERTISEMENT

Sai dai ya ki amsa laifin da ake tuhumarsa da shi.

Watanni uku da suka gabata shi da magoya bayansa sun mamaye Majalisar don “tabbatar da” hukuncin soke dakatarwar da majalisar ta yi masa.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

A watan Satumba, 2022 ne majalisar ta dakatar da dan majalisar da wani mutum bisa zargin tauye hakki na majalisar dokokin jihar.

An kuma tsige Kadiri a matsayin mataimakin kakakin majalisar.

Sai dai wata babbar kotun Jihar Ogun da ta zauna a Abeokuta a watan Maris ta soke dakatarwar da aka yi wa Kadiri tare da sauran.

A ranar Talatar da ta gabata ne aka yi zargin cewa ya rufe babbar kofar harabar majalisar inda ya dage cewa dole ne a bar shi ya ci gaba da zama dan majalisar dokokin jihar domin ya ci gaba da gudanar da aikinsa kamar yadda kotu ta umarce shi.

An ga jami’an tsaro suna lallashin dan majalisar tare da shiga tsakani.

An dai ga tsohon mataimakin kakakin ne zaune a cikin motarsa yana latsa wayarsa, yayin da lamarin ya ci tura.

Dan sanda mai gabatar da kara, Lawrence Olu-Balogun, ya shaida wa kotun cewa wanda ake kara ya aikata laifin ne a ranar 25 ga watan Maris da misalin karfe 8:40 na safe a harabar majalisar da ke Oke-Mosan.

Olu-Balogun ya ce wanda ake kara ya shiga harabar majalisar inda ya yi barazana ga rayuwar ‘yan majalisar da sauran jami’an da ke ciki.

Ya kuma kara da cewa wanda ake tuhumar ya kuma yi amfani da motarsa wajen tare kofar shiga majalisar.

Lauyan mai shigar da karar ya ce tsohon dan majalisar ya gudanar da kansa ne ta hanyar da za ta iya haifar da kawo matsala ga zaman lafiya ta hanyar kai hari wanda ya kawo cikas ga tsarin samar da doka a majalisar.

Olu-Balogun ya bayyana cewa an dakatar da wanda ake tuhuma tun watan Maris din 2022, amma ya yi ikirarin cewa ya samu hukunci daga wata babbar kotu a Ogun, inda ya nemi ya koma ofishinsa.

Ya kara da cewa a lokacin da wanda ake kara ya isa zauren majalisar, jami’an tsaron da ke kofar majalisar sun hana shi shiga harabar.

A cewar masa, laifukan sun ci karo da sashe na 86(1) da 249(D) na kundin laifuffuka na Ogun na shekarar 2006.

Babban alkalin kotun, Misis M.O. Osinbajo, ta ba da belinsa.

Alkalin kotun ta dage ci gaba da sauraren karar har zuwa ranar 1 ga watan Yuni.

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
Next Post
Za Mu Yi Nazarin Rahoton Mika Mulki Da Ganduje Ya Ba Mu -NNPP

Za Mu Yi Nazarin Rahoton Mika Mulki Da Ganduje Ya Ba Mu -NNPP

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.