ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gurfanar Da Tsohon Mataimakin Kakakin Majalisar Ogun Kan Zargin Tada Zaune-Tsaye

by Sadiq
3 years ago
Ogun

An gurfanar da tsohon mataimakin kakakin majalisar dokokin Jihar Ogun, Oludare Kadiri a gaban wata kotun majistare da ke Abeokuta bisa zargin barazana ga rayuwa da kuma tada zaune-tsaye.

Hakan dai ya biyo bayan wani sabani da aka samu yi a ranar Talata a zauren majalisar yayin da Kadiri ya toshe babbar kofar shiga harabar majalisar.

  • Kwana 5 Ga Rantsuwa: Waiwaye Kan Rawar Da Matan Shugabannin Kasa Suka Taka A Baya
  • Tony Blair Ya Ziyarci Tinubu A Abuja

An kama Kadiri, mai shekaru 54, daga baya kuma aka tuhume shi da laifuka biyu na barazana ga rayuwa da kuma haddasa rashin zaman lafiya.

ADVERTISEMENT

Sai dai ya ki amsa laifin da ake tuhumarsa da shi.

Watanni uku da suka gabata shi da magoya bayansa sun mamaye Majalisar don “tabbatar da” hukuncin soke dakatarwar da majalisar ta yi masa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

A watan Satumba, 2022 ne majalisar ta dakatar da dan majalisar da wani mutum bisa zargin tauye hakki na majalisar dokokin jihar.

An kuma tsige Kadiri a matsayin mataimakin kakakin majalisar.

Sai dai wata babbar kotun Jihar Ogun da ta zauna a Abeokuta a watan Maris ta soke dakatarwar da aka yi wa Kadiri tare da sauran.

A ranar Talatar da ta gabata ne aka yi zargin cewa ya rufe babbar kofar harabar majalisar inda ya dage cewa dole ne a bar shi ya ci gaba da zama dan majalisar dokokin jihar domin ya ci gaba da gudanar da aikinsa kamar yadda kotu ta umarce shi.

An ga jami’an tsaro suna lallashin dan majalisar tare da shiga tsakani.

An dai ga tsohon mataimakin kakakin ne zaune a cikin motarsa yana latsa wayarsa, yayin da lamarin ya ci tura.

Dan sanda mai gabatar da kara, Lawrence Olu-Balogun, ya shaida wa kotun cewa wanda ake kara ya aikata laifin ne a ranar 25 ga watan Maris da misalin karfe 8:40 na safe a harabar majalisar da ke Oke-Mosan.

Olu-Balogun ya ce wanda ake kara ya shiga harabar majalisar inda ya yi barazana ga rayuwar ‘yan majalisar da sauran jami’an da ke ciki.

Ya kuma kara da cewa wanda ake tuhumar ya kuma yi amfani da motarsa wajen tare kofar shiga majalisar.

Lauyan mai shigar da karar ya ce tsohon dan majalisar ya gudanar da kansa ne ta hanyar da za ta iya haifar da kawo matsala ga zaman lafiya ta hanyar kai hari wanda ya kawo cikas ga tsarin samar da doka a majalisar.

Olu-Balogun ya bayyana cewa an dakatar da wanda ake tuhuma tun watan Maris din 2022, amma ya yi ikirarin cewa ya samu hukunci daga wata babbar kotu a Ogun, inda ya nemi ya koma ofishinsa.

Ya kara da cewa a lokacin da wanda ake kara ya isa zauren majalisar, jami’an tsaron da ke kofar majalisar sun hana shi shiga harabar.

A cewar masa, laifukan sun ci karo da sashe na 86(1) da 249(D) na kundin laifuffuka na Ogun na shekarar 2006.

Babban alkalin kotun, Misis M.O. Osinbajo, ta ba da belinsa.

Alkalin kotun ta dage ci gaba da sauraren karar har zuwa ranar 1 ga watan Yuni.

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Za Mu Yi Nazarin Rahoton Mika Mulki Da Ganduje Ya Ba Mu -NNPP

Za Mu Yi Nazarin Rahoton Mika Mulki Da Ganduje Ya Ba Mu -NNPP

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.