ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gurfanar Da Wani Mashawarcin Bogi Bisa Zargin Zambar Naira 600,000

by Umar Faruk Birnin Kebbi
1 year ago
Gurfanar

A ranar Litinin ne rundunar ‘yansandan ta gurfanar da wani mai ba da shawara kan harkokin ilimi na jami’ar Tai Solarin Sadiku Rasaki na bogi, mai shekaru 47 a gaban kuliya, da laifin karbar kudi Naira 600,000 daga hannun mahaifin wani dalibin makarantar.

An gurfanar da Rasaki a gaban kotun majistare da ke Igbosere da ke Ebute-Metta, a kan laifuka uku da suka hada da karba, sata, wanda ‘yan sanda suka ambata masa.

  • Mu Kare Daraja Muhallinmu, Kuma Mu Kare Nijeriya Daga Labaran Bogi – Minista
  • JAMB Ta Bankaɗo Ɗalibai 3000 Da Suka Kammala Karatun Bogi

Dansanda mai gabatar da kara, sufeta Cyriacus Osuji, ya shaida wa kotun cewa wanda ake tuhumar ya aikata laifin ne a wani lokaci a watan Satumban 2023, a Legas.

ADVERTISEMENT

Ya ce, Rasaki, wanda ake zargin ya karbi kudi Naira 600,000, daga hannun wani Mista James Oyeleke, bisa zargin taimakawa dansa, Nathaniel Oyeleke, wajen saukaka sakin takardar shaidar makarantarsa.

Osuji ya ce kudaden da aka karba mallakin mahaifin dalibin Jami’ar ilimi ce ta Tai Solarin, Mista Oyeleke.

LABARAI MASU NASABA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

Mai gabatar da kara ya ci gaba da shaida wa kotun cewa Rasaki ya kwaikwayi hanyar gabatar da kansa ga wanda ya shigar da karar a matsayin mai ba da shawara kan ilimi ga jami’ar.

A cewar mai gabatar da kara, laifukan da aka aikata sun sabawa sashe na 314 da kuma hukunci a karkashin sashe na 287 da 383 na dokokin laifuka na Jihar Legas 2015.

Rasaki ya musanta zargin da ake masa.

Sai dai alkalin kotun mai shari’a Oluwatosin Erinle ya bayar da belinsa a kan kudi Naira 300,000, tare da mutum biyu da za su tsaya masa.

Kotun ta ce dole ne daya daga cikin wadanda za su tsaya masa ya zama mutum dan uwa ne na jini, kuma ya nuna shaidar biyan haraji ga gwamnatin Jihar Legas, takardar banki na watanni shida.

Alkalin kotun ya kuma ba da umarnin a tantance adireshin wadanda za su tsaya masu.

An dage sauraron karar har zuwa ranar 30 ga Yuli, 2024, don ci gaba da zaman.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
Kotu Da Ɗansanda

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
Kotu Da Ɗansanda

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
Next Post
Chelsea Na Neman Sabon Gola Domin Tunkarar Sabuwar Kakar Wasa Ta Bana 

Chelsea Na Neman Sabon Gola Domin Tunkarar Sabuwar Kakar Wasa Ta Bana 

LABARAI MASU NASABA

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

November 13, 2025
Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25

November 13, 2025
Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

November 13, 2025
Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

November 13, 2025
‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

November 13, 2025
Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.