• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kaddamar Da Kungiyar Samar Da Tsarin Ci Gaban Jihar Kano

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Labarai
0
An Kaddamar Da Kungiyar Samar Da Tsarin Ci Gaban Jihar Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu masu kishin Jihar Kano sun kaddamar da wata kungiya mai suna “Kano Charter” wadda za ta dinga bibiya tare da sanya ido a kan bukatun da al’ummar Jihar Kano suke da su na ci gaba da bunkasar tattalin aziki.

A yayin taron kaddamar da kungiyar wanda aka yi a Cibiyar Bunkasa Fasahar Sadarwa da Ci Gaban Al’umma (CITAD) da ke Kano ya samu halartar manyan mutane masu kishin Jihar Kano daga fannoni daban-daban na fadin jihar.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Kammala Aikin Gadar Neja Ta Biyu
  • Yobe Ta Arewa: Machina Ya Sake Samun Nasara Yayin Da Kotu Ta Kori Karar Da Aka Sake Shigarwa A Kansa 

A jawabinsa, Dokta Isa Ahmed, wanda shi ne shugaban gamayyar, ya bayyana cewa wannan sabon tsari ne da aka shigo da shi domin ganin an dora Jihar Kano a kan turba mai dorewa duk da cewa a shekarun baya ma akwai irin wannan gamayyar.

Ya kara da cewa Kano gari ne mai cike da tarin albarkatu daban-daban saboda haka akwai bukatar samun tsari mai inganci wanda zai dora duk shugaban da zai zo a kan tsarin da zai kawo ci gaba mai dorewa a jihar.

Shi ma a yayin da yake jawabinsa, Farfesa Nu’uman Habib Muhammad da ke Jami’ar Bayero ta Kano, ya bayyana cewa dole sai an samu shugaban da zai kasance mai cikakkiyar biyayya da girmama tanade-tanaden tsarin mulki na kasa da addini da wanda zai samar da cin gashin kai da bangarorin shari’a da bijro da tsari mai saukin aiwatarwa.

Labarai Masu Nasaba

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

Sannan ya ce Kano tana bukatar samar da hanyoyin kudin shiga da fitar da tsarin kyautata rayuwar al’umma samar da tsarin rage kashe kudaden al’umma da kuma biyayya ga tsare-tsaren kundin mulkin kasa.

Taron ya samu halartar shugaban Cibiyar Bunkasa Fasahar Sadarwa da Ci Gaban Al’umma  (CITAD), Injinya Yunusa Zakari Ya’u da Prof. Baffa Aliyu Umar da Dokta Gausu Ahmad da Dokta Sa’idu Ahmad Dukawa da Dokta Bala Muhammad (Adaidaita Sahu) da Dokta Dalhatu Sani Yola da Farouk Lawal Yola da Nasidi Abdullahi da Ibrahim Ado Kurawa da Farouk Ibrahim Mukhtar da Umar Muhammad Jalo da Ibrahim Sadauki Kabara da Aliyu Isma’il diso da Tafada A. Babba da Ummi Tanko Yakasai da Amina Aminu Dantata da Auwalu Muhammad Umar da Nura Shafi’u da kuma Idris Makama Unguwar Gini da sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci Gaban Al'ummaCitadGamnayar KungiyoyiJihar KanoShugaba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Kammala Aikin Gadar Neja Ta Biyu

Next Post

Ambaliyar Ruwa: Ku Kwashe Jama’ar Da Suke Zaune A Yankunan Magudanun Ruwa — Sadiya Farouq

Related

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS
Labarai

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

3 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

5 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

5 hours ago
Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan
Labarai

Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

6 hours ago
Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja
Tsaro

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

6 hours ago
Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri
Labarai

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

8 hours ago
Next Post
Ambaliyar Ruwa: Ku Kwashe Jama’ar Da Suke Zaune A Yankunan Magudanun Ruwa — Sadiya Farouq

Ambaliyar Ruwa: Ku Kwashe Jama'ar Da Suke Zaune A Yankunan Magudanun Ruwa — Sadiya Farouq

LABARAI MASU NASABA

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

June 27, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

June 27, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

June 27, 2025
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

June 27, 2025
WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

June 27, 2025
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

June 27, 2025
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

June 27, 2025
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

June 27, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

June 27, 2025
Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.