• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kaddamar Da Kungiyar Samar Da Tsarin Ci Gaban Jihar Kano

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Labarai
0
An Kaddamar Da Kungiyar Samar Da Tsarin Ci Gaban Jihar Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu masu kishin Jihar Kano sun kaddamar da wata kungiya mai suna “Kano Charter” wadda za ta dinga bibiya tare da sanya ido a kan bukatun da al’ummar Jihar Kano suke da su na ci gaba da bunkasar tattalin aziki.

A yayin taron kaddamar da kungiyar wanda aka yi a Cibiyar Bunkasa Fasahar Sadarwa da Ci Gaban Al’umma (CITAD) da ke Kano ya samu halartar manyan mutane masu kishin Jihar Kano daga fannoni daban-daban na fadin jihar.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Kammala Aikin Gadar Neja Ta Biyu
  • Yobe Ta Arewa: Machina Ya Sake Samun Nasara Yayin Da Kotu Ta Kori Karar Da Aka Sake Shigarwa A Kansa 

A jawabinsa, Dokta Isa Ahmed, wanda shi ne shugaban gamayyar, ya bayyana cewa wannan sabon tsari ne da aka shigo da shi domin ganin an dora Jihar Kano a kan turba mai dorewa duk da cewa a shekarun baya ma akwai irin wannan gamayyar.

Ya kara da cewa Kano gari ne mai cike da tarin albarkatu daban-daban saboda haka akwai bukatar samun tsari mai inganci wanda zai dora duk shugaban da zai zo a kan tsarin da zai kawo ci gaba mai dorewa a jihar.

Shi ma a yayin da yake jawabinsa, Farfesa Nu’uman Habib Muhammad da ke Jami’ar Bayero ta Kano, ya bayyana cewa dole sai an samu shugaban da zai kasance mai cikakkiyar biyayya da girmama tanade-tanaden tsarin mulki na kasa da addini da wanda zai samar da cin gashin kai da bangarorin shari’a da bijro da tsari mai saukin aiwatarwa.

Labarai Masu Nasaba

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Sannan ya ce Kano tana bukatar samar da hanyoyin kudin shiga da fitar da tsarin kyautata rayuwar al’umma samar da tsarin rage kashe kudaden al’umma da kuma biyayya ga tsare-tsaren kundin mulkin kasa.

Taron ya samu halartar shugaban Cibiyar Bunkasa Fasahar Sadarwa da Ci Gaban Al’umma  (CITAD), Injinya Yunusa Zakari Ya’u da Prof. Baffa Aliyu Umar da Dokta Gausu Ahmad da Dokta Sa’idu Ahmad Dukawa da Dokta Bala Muhammad (Adaidaita Sahu) da Dokta Dalhatu Sani Yola da Farouk Lawal Yola da Nasidi Abdullahi da Ibrahim Ado Kurawa da Farouk Ibrahim Mukhtar da Umar Muhammad Jalo da Ibrahim Sadauki Kabara da Aliyu Isma’il diso da Tafada A. Babba da Ummi Tanko Yakasai da Amina Aminu Dantata da Auwalu Muhammad Umar da Nura Shafi’u da kuma Idris Makama Unguwar Gini da sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci Gaban Al'ummaCitadGamnayar KungiyoyiJihar KanoShugaba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Kammala Aikin Gadar Neja Ta Biyu

Next Post

Ambaliyar Ruwa: Ku Kwashe Jama’ar Da Suke Zaune A Yankunan Magudanun Ruwa — Sadiya Farouq

Related

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

28 minutes ago
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

2 hours ago
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu
Labarai

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

3 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

5 hours ago
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

8 hours ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

8 hours ago
Next Post
Ambaliyar Ruwa: Ku Kwashe Jama’ar Da Suke Zaune A Yankunan Magudanun Ruwa — Sadiya Farouq

Ambaliyar Ruwa: Ku Kwashe Jama'ar Da Suke Zaune A Yankunan Magudanun Ruwa — Sadiya Farouq

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.