ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kaddamar Da Kungiyar Samar Da Tsarin Ci Gaban Jihar Kano

by Abba Ibrahim Wada
4 years ago
Kano

Wasu masu kishin Jihar Kano sun kaddamar da wata kungiya mai suna “Kano Charter” wadda za ta dinga bibiya tare da sanya ido a kan bukatun da al’ummar Jihar Kano suke da su na ci gaba da bunkasar tattalin aziki.

A yayin taron kaddamar da kungiyar wanda aka yi a Cibiyar Bunkasa Fasahar Sadarwa da Ci Gaban Al’umma (CITAD) da ke Kano ya samu halartar manyan mutane masu kishin Jihar Kano daga fannoni daban-daban na fadin jihar.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Kammala Aikin Gadar Neja Ta Biyu
  • Yobe Ta Arewa: Machina Ya Sake Samun Nasara Yayin Da Kotu Ta Kori Karar Da Aka Sake Shigarwa A Kansa 

A jawabinsa, Dokta Isa Ahmed, wanda shi ne shugaban gamayyar, ya bayyana cewa wannan sabon tsari ne da aka shigo da shi domin ganin an dora Jihar Kano a kan turba mai dorewa duk da cewa a shekarun baya ma akwai irin wannan gamayyar.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa Kano gari ne mai cike da tarin albarkatu daban-daban saboda haka akwai bukatar samun tsari mai inganci wanda zai dora duk shugaban da zai zo a kan tsarin da zai kawo ci gaba mai dorewa a jihar.

Shi ma a yayin da yake jawabinsa, Farfesa Nu’uman Habib Muhammad da ke Jami’ar Bayero ta Kano, ya bayyana cewa dole sai an samu shugaban da zai kasance mai cikakkiyar biyayya da girmama tanade-tanaden tsarin mulki na kasa da addini da wanda zai samar da cin gashin kai da bangarorin shari’a da bijro da tsari mai saukin aiwatarwa.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Sannan ya ce Kano tana bukatar samar da hanyoyin kudin shiga da fitar da tsarin kyautata rayuwar al’umma samar da tsarin rage kashe kudaden al’umma da kuma biyayya ga tsare-tsaren kundin mulkin kasa.

Taron ya samu halartar shugaban Cibiyar Bunkasa Fasahar Sadarwa da Ci Gaban Al’umma  (CITAD), Injinya Yunusa Zakari Ya’u da Prof. Baffa Aliyu Umar da Dokta Gausu Ahmad da Dokta Sa’idu Ahmad Dukawa da Dokta Bala Muhammad (Adaidaita Sahu) da Dokta Dalhatu Sani Yola da Farouk Lawal Yola da Nasidi Abdullahi da Ibrahim Ado Kurawa da Farouk Ibrahim Mukhtar da Umar Muhammad Jalo da Ibrahim Sadauki Kabara da Aliyu Isma’il diso da Tafada A. Babba da Ummi Tanko Yakasai da Amina Aminu Dantata da Auwalu Muhammad Umar da Nura Shafi’u da kuma Idris Makama Unguwar Gini da sauransu.

Kano
Abba Ibrahim Wada
+ postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Har Yanzu Nijeriya Tana Fatan Zuwa Kofin Duniya Na 2026
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Mece Ce Matsalar Real Madrid? 
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Ko Ka San Dalilin Da Zai Bai Wa Nijeriya Damar Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Next Post
Ambaliyar Ruwa: Ku Kwashe Jama’ar Da Suke Zaune A Yankunan Magudanun Ruwa — Sadiya Farouq

Ambaliyar Ruwa: Ku Kwashe Jama'ar Da Suke Zaune A Yankunan Magudanun Ruwa — Sadiya Farouq

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.