ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kammala Canja Fasalin Gasar Cin Kofin Zakarun Turai

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
UEFA

Hukumar kwallon kafa ta Nahiyar Turai, UEFA ta sanar da sauye-sauyen da za a yi a gasar cin kofin zakarun Turai daga kakar wasa mai zuwa bayan daukar shekara da shekaru ana shirye-shirye.

Muhimmin sauyi da kwamitin zartarwa na UEFA ya sanar shi ne ficewa daga tsarin matakin rukuni da ake yi yanzu sannan a halin yanzu matakin rukuni na gasar zakarun Turai ya kunshi kungiyoyi 32 da aka raba cikin rukunai takwas inda kowanne rukuni ke kunshe da kungiyoyi hudu. Daga kakar wasa ta 2024/25, kungiyoyi 36 ne za su shiga gasar cin kofin zakarun Turai (tsohon matakin rukuni), wanda zai ba wa wasu kungiyoyi hudu damar fafatawa da kungiyoyin da suka fi fice a Turai.

  • Ba Za Mu Lamunci Cin Zarafin Wani Da Sunan Tafsiri Ba – Gwamnatin Kaduna
  • Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Tallafawa Matakan Siyasa A Sudan

Kungiyoyi 36 ne za su shiga gasar Lig guda daya wadda dukkanin kungiyoyin za su kasance a teburi daya, sannan a karkashin sabon tsarin, kungiyoyi za su buga wasanni takwas a sabon matakin gasar (tsohon matakin rukuni).

ADVERTISEMENT

Za su fafata da kungiyoyi daban-daban guda takwas, inda za su buga rabin wadannan wasannin a gida, rabinsu kuma a waje. Domin tantance kungiyoyin da za su fafata da juna, da farko za a sanya kungiyoyin a cikin tukwane guda hudu sannan za a fitar da kowace kungiya domin ta yi wasa da abokan hamayya biyu daga kowacce tukunya, inda za a yi wasa daya da kungiya daga kowace tukunya a gida, daya kuma a waje.

Kungiyoyi takwas na farko a teburin za su tsallaka zuwa zagaye na 16 kai tsaye, yayin da kungiyoyin da suka kare a matsayi na 9 zuwa na 24 za su fafata a cike gurbi don samun damar ketarawa zuwa zagaye na ‘yan 16 na karshe a gasar sai kungiyoyin da suka kare a matsayi na 25 zuwa kasa za a fitar da su, ba tare da samun damar shiga gasar Europa League ba.

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya 2026 Zai Zama Na Ƙarshe A Wuri Na – Ronaldo 

‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kofin Duniya 2026 Zai Zama Na Ƙarshe A Wuri Na – Ronaldo 
Wasanni

Kofin Duniya 2026 Zai Zama Na Ƙarshe A Wuri Na – Ronaldo 

November 11, 2025
‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina
Wasanni

‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

November 11, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL
Wasanni

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sace Daliban Tsangaya 15 A Sakkwato

'Yan Bindiga Sun Sace Daliban Tsangaya 15 A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

November 12, 2025
Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

November 12, 2025
Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

November 12, 2025
Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

November 12, 2025
Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025
CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.