• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Karrama Xi Da Lambar Yabo Ta Afirka Ta Kudu, Sannan Xi da Cyril Ramaphosa Sun Gana Da ’Yan Jaridu

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
An Karrama Xi Da Lambar Yabo Ta Afirka Ta Kudu, Sannan Xi da Cyril Ramaphosa Sun Gana Da ’Yan Jaridu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Talatar nan ne shugaban kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa, ya karrama takwaransa na kasar Sin Xi Jinping da lambar yabo ta Afirka ta Kudu.

Da yake jawabi a wajen bikin, Xi ya ce, dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare dake tsakanin Sin da Afirka ta Kudu ta shiga muhimmin lokaci, yayin da amincewa da juna ta fuskar siyasa ke ci gaba da zurfafa, kuma hadin gwiwar moriyar juna a aikace a fannoni daban-daban ta haifar da sakamako mai gamsarwa.

  • Shin Japan Biris Za Ta Yi Da Hakkin Al’ummarta Da Na Makwabtaka?

Ya kara da cewa, kasashen biyu sun ci gaba da yin hadin gwiwa a harkoki na kasa da kasa, wanda ya taimaka wajen ci gaba da ma farfadowarsu, tare da ba da gagarumar gudummawa wajen kiyaye moriyar kasashe masu tasowa.

Ya kuma bayyana cewa, zai martaba wannan karramawa, wadda ke nuna alakar abokantaka a tsakanin al’ummomin kasashen biyu, Xi ya kuma yi alkawarin kara himmantuwa wajen ci gaba da raya dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka ta Kudu.

Sannan a yammacin yau Talatar nan ne shugaba Xi Jinping na kasar Sin da takwaransa na kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa suka gana da manema labaru bayan shawarwarin da suka yi a fadar shugaban Afirka ta Kudu da ke birnin Pretoria.

Labarai Masu Nasaba

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Xi ya bayyana cewa, a bana aka cika shekaru 25 da kulla huldar diplomasiyya a tsakanin Sin da Afirka ta Kudu. Dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka ta Kudu ta samu ci gaba mai zurfi a cikin shekaru 25 da suka gabata, inda amincewa da juna bisa manyan tsare-tsare ya kai wani sabon matsayi.

Haka kuma dangantakar da ke tsakanin Sin da Afirka ta Kudu ta zarce alakar sassan biyu, har ma ta yi tasiri a duniya. Dazun nan shugaba Ramaphosa da Xi sun yi shawarwari a tsakaninsu, inda suka yi musayar ra’ayoyi dangane da ci gaban huldar da ke tsakanin kasashen 2 a sabon zamani da kuma al’amuran kasa da kasa da na shiyya-shiyya wadanda suka jawo hankalinsu duka, tare da cimma daidaito mai muhimmanci.

A nasa bangaren, shugaba Ramaphosa ya ce, dukkan shugabannin 2 sun amince da zurfafa hadin gwiwar kasashen 2 a fannonin ciniki da zuba jari, da fadada hadin kan moriyar juna a fannonin ababen more rayuwar jama’a, yawon bude ido, ba da ilmi, tattalin arziki na zamani da dai sauransu, tare da kara taimakawa juna a manyan al’amuran kasa da kasa da na shiyya-shiyya. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bukaci Japan Da Ta Dakatar Da Mummunar Shawarar Da Ta Yanke Ta Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku

Next Post

Rikici Ya Kaure Tsakanin ‘Yan Bindiga A Benuwe, Sun Fara Kashe Juna

Related

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

17 minutes ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

2 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

2 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

6 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

8 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

8 hours ago
Next Post
Rikici Ya Kaure Tsakanin ‘Yan Bindiga A Benuwe, Sun Fara Kashe Juna

Rikici Ya Kaure Tsakanin 'Yan Bindiga A Benuwe, Sun Fara Kashe Juna

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.