• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe Makiyaya 6, Wasu Sun Bace Bat A Filato

by Khalid Idris Doya
3 years ago

Wasu makiyaya guda shida sun rigamu zuwa gidan gaskiya a yayin da wasu karin bakwai suka bace bat a kauyukan Mongi da Langai da ke karamar hukumar Mangu a jihar Filato.

Shugaban kungiyar Fulani (MACBAN) a jihar Filato, Malam Nura Abdullahi shi ne ya tabbatar da hakan, ya yi zargin cewa wasu mambobin kungiyar ‘yan banga da ke Bauchi ne a ranar 22 ga watan Yulin 2022 suka shiga cikin kauyukan tare da kama Fulanin hadi da kai su daji da kashe su.

  • Matsin Rayuwa: Za A Rage Farashin Man Fetur A Afrika Ta Kudu
  • NDLEA Ta Kwace Tiramol Miliyan 2.7 A Legas

Shugaban na MACBAN ya kara da cewa mambobinsu Fulani 13 aka kama, inda aka samu gawar shiga daga cikin yayin da bakwai kuma ba a san inda suke ba har yanzu.

Ya ce, “Daga ranar Lahadi 23 ga watan Yuli zuwa ranar Lahadi 31 ga watan Yuli mun binne mutum shida. Dukkanin wadanda aka kashe ba su san hawa ko sauka ba. Sannan har yanzu hudu kuma sun bace.

“Biyu daga cikin wadanda aka kashe sun fito ne daga Mongi sai kuma hudu ‘yan kauyen Langai. Daga cikin cikin wadanda aka kashe ya kammala jami’a sai kuma a cikinsu akwai dan shekara 65 dukka an kashe ba tare sun yi laifin komai ba.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

“Wannan ba abu ne da za a lamunta ba. Ta’addanci ne marar dadi. Daukan hukuncin kisa lallai ba abu ne da ya kamata jama’a suke yi ba. Idan ana zarginsu da laifin garkuwa da mutane, kamata ya yi a kaisu kotu ta bincika ta hukuntasu ba wai wadanda suka kama su din su zartar musu kawai da hukuncin kisa ba.

“Ya kamata ne kotu ta bincika ta tabbatar da abun da ake zarginsu kafin a kai ga yanke musu hukunci.

“Bayan da aka kashe, wadanda suka kashe su din sun sace musu kadarorinsu da kudadensu. Sun kwashe musu Mashina. Muna kira ga hukumomin tsaro da su dauki mataki kan wannan lamarin. Na kuma sanar da GOC 3 Division kan wannan batun.”

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi, SP Ahmed Mohammed Wakil, ya ce rundunar su tana sane da faruwar lamarin sai dai kisan ya faru ne ba a karkashin ikonsu ba.

Ya ce, “Ban san cikakken abun da ya faru ba. Ina tunanin rundunar ‘yan sandan reshen jihar Filato ne suke da alhakin yin magana kan abun da ya faru.

“Ba mu da masaniya kan kungiyar da suke zargi. Idan sun san mutunan da suka kashe musu mambobi su nuna mana su. Don an ajiye gawarwakin wadanda aka kashe a Bauchi ba shine yake nufin an kashe a Bauchi ba ne.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 
Labarai

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

October 20, 2025
Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

October 20, 2025
Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba
Labarai

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

October 20, 2025
Next Post
Da Dumi-Dumi: ASUU Ta Tsawaita Yajin Aikinta Zuwa Makonni 4

Da Dumi-Dumi: ASUU Ta Tsawaita Yajin Aikinta Zuwa Makonni 4

LABARAI MASU NASABA

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

October 20, 2025
Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

October 20, 2025
Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

October 20, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.