• English
  • Business News
Saturday, May 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe Makiyaya 6, Wasu Sun Bace Bat A Filato

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
An Kashe Makiyaya 6, Wasu Sun Bace Bat A Filato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu makiyaya guda shida sun rigamu zuwa gidan gaskiya a yayin da wasu karin bakwai suka bace bat a kauyukan Mongi da Langai da ke karamar hukumar Mangu a jihar Filato.

Shugaban kungiyar Fulani (MACBAN) a jihar Filato, Malam Nura Abdullahi shi ne ya tabbatar da hakan, ya yi zargin cewa wasu mambobin kungiyar ‘yan banga da ke Bauchi ne a ranar 22 ga watan Yulin 2022 suka shiga cikin kauyukan tare da kama Fulanin hadi da kai su daji da kashe su.

  • Matsin Rayuwa: Za A Rage Farashin Man Fetur A Afrika Ta Kudu
  • NDLEA Ta Kwace Tiramol Miliyan 2.7 A Legas

Shugaban na MACBAN ya kara da cewa mambobinsu Fulani 13 aka kama, inda aka samu gawar shiga daga cikin yayin da bakwai kuma ba a san inda suke ba har yanzu.

Ya ce, “Daga ranar Lahadi 23 ga watan Yuli zuwa ranar Lahadi 31 ga watan Yuli mun binne mutum shida. Dukkanin wadanda aka kashe ba su san hawa ko sauka ba. Sannan har yanzu hudu kuma sun bace.

“Biyu daga cikin wadanda aka kashe sun fito ne daga Mongi sai kuma hudu ‘yan kauyen Langai. Daga cikin cikin wadanda aka kashe ya kammala jami’a sai kuma a cikinsu akwai dan shekara 65 dukka an kashe ba tare sun yi laifin komai ba.

Labarai Masu Nasaba

Mutum 3 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Bama-bamai Suka Tashi A Hanyar Borno

Hukuma Ta Haramta Bikin Ranar Kauyawa A Kano

“Wannan ba abu ne da za a lamunta ba. Ta’addanci ne marar dadi. Daukan hukuncin kisa lallai ba abu ne da ya kamata jama’a suke yi ba. Idan ana zarginsu da laifin garkuwa da mutane, kamata ya yi a kaisu kotu ta bincika ta hukuntasu ba wai wadanda suka kama su din su zartar musu kawai da hukuncin kisa ba.

“Ya kamata ne kotu ta bincika ta tabbatar da abun da ake zarginsu kafin a kai ga yanke musu hukunci.

“Bayan da aka kashe, wadanda suka kashe su din sun sace musu kadarorinsu da kudadensu. Sun kwashe musu Mashina. Muna kira ga hukumomin tsaro da su dauki mataki kan wannan lamarin. Na kuma sanar da GOC 3 Division kan wannan batun.”

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi, SP Ahmed Mohammed Wakil, ya ce rundunar su tana sane da faruwar lamarin sai dai kisan ya faru ne ba a karkashin ikonsu ba.

Ya ce, “Ban san cikakken abun da ya faru ba. Ina tunanin rundunar ‘yan sandan reshen jihar Filato ne suke da alhakin yin magana kan abun da ya faru.

“Ba mu da masaniya kan kungiyar da suke zargi. Idan sun san mutunan da suka kashe musu mambobi su nuna mana su. Don an ajiye gawarwakin wadanda aka kashe a Bauchi ba shine yake nufin an kashe a Bauchi ba ne.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FadaFilatoKisaMakiyayaRikici
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsin Rayuwa: Za A Rage Farashin Man Fetur A Afrika Ta Kudu

Next Post

Da Dumi-Dumi: ASUU Ta Tsawaita Yajin Aikinta Zuwa Makonni 4

Related

Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno
Manyan Labarai

Mutum 3 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Bama-bamai Suka Tashi A Hanyar Borno

6 hours ago
Hukuma Ta Haramta Bikin Ranar Kauyawa A Kano
Labarai

Hukuma Ta Haramta Bikin Ranar Kauyawa A Kano

8 hours ago
Dalilin Ƴansandan Kano Na Tsare Wasu Awaki
Labarai

Dalilin Ƴansandan Kano Na Tsare Wasu Awaki

9 hours ago
Ƙungiyar Fulani Makiyaya Ta Nuna Damuwarta Na Ɓacewar Mataimakin Shugabanta
Labarai

Ƙungiyar Fulani Makiyaya Ta Nuna Damuwarta Na Ɓacewar Mataimakin Shugabanta

10 hours ago
Hisbah Ta Rufe Otal, Ta Kwato Ƙwalaben Giya 209 A Yobe
Labarai

Hisbah Ta Rufe Otal, Ta Kwato Ƙwalaben Giya 209 A Yobe

12 hours ago
Babu Wani Dan Jarida Da Aka Hana Shiga Taron Gwamnonin Arewa – CPS Ibrahim Musa
Labarai

Babu Wani Dan Jarida Da Aka Hana Shiga Taron Gwamnonin Arewa – CPS Ibrahim Musa

12 hours ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: ASUU Ta Tsawaita Yajin Aikinta Zuwa Makonni 4

Da Dumi-Dumi: ASUU Ta Tsawaita Yajin Aikinta Zuwa Makonni 4

LABARAI MASU NASABA

Masana Kimiyya Na Kasar Sin Sun Gano Wata Sabuwar Hallita A Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar 

Masana Kimiyya Na Kasar Sin Sun Gano Wata Sabuwar Hallita A Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar 

May 17, 2025
Crystal Palace Ta Lashe Kofin FA Karon Farko, Ta Doke Manchester City 1-0

Crystal Palace Ta Lashe Kofin FA Karon Farko, Ta Doke Manchester City 1-0

May 17, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 17, 2025
Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taro Na 34 Na Kasashen Larabawa

Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taro Na 34 Na Kasashen Larabawa

May 17, 2025
Jami’ar FUDMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina

Jami’ar FUDMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina

May 17, 2025
Rokar Kasuwanci Ta Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 6 Zuwa Sararin Samaniya

Rokar Kasuwanci Ta Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 6 Zuwa Sararin Samaniya

May 17, 2025
Gidan Adana Kayayyakin Tarihi Na Amurka Ya Mayarwa Kasar Sin Rubuce-rubucen Hannu Masu Daraja Na Lokacin Yake-yake A Kasar

Gidan Adana Kayayyakin Tarihi Na Amurka Ya Mayarwa Kasar Sin Rubuce-rubucen Hannu Masu Daraja Na Lokacin Yake-yake A Kasar

May 17, 2025
Bude Kofar Kasar Sin Dama Ce Ga Duniya Har Abada

Bude Kofar Kasar Sin Dama Ce Ga Duniya Har Abada

May 17, 2025
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Mutum 3 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Bama-bamai Suka Tashi A Hanyar Borno

May 17, 2025
Hukuma Ta Haramta Bikin Ranar Kauyawa A Kano

Hukuma Ta Haramta Bikin Ranar Kauyawa A Kano

May 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.