ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe Makiyaya 6, Wasu Sun Bace Bat A Filato

by Khalid Idris Doya
4 years ago

Wasu makiyaya guda shida sun rigamu zuwa gidan gaskiya a yayin da wasu karin bakwai suka bace bat a kauyukan Mongi da Langai da ke karamar hukumar Mangu a jihar Filato.

Shugaban kungiyar Fulani (MACBAN) a jihar Filato, Malam Nura Abdullahi shi ne ya tabbatar da hakan, ya yi zargin cewa wasu mambobin kungiyar ‘yan banga da ke Bauchi ne a ranar 22 ga watan Yulin 2022 suka shiga cikin kauyukan tare da kama Fulanin hadi da kai su daji da kashe su.

  • Matsin Rayuwa: Za A Rage Farashin Man Fetur A Afrika Ta Kudu
  • NDLEA Ta Kwace Tiramol Miliyan 2.7 A Legas

Shugaban na MACBAN ya kara da cewa mambobinsu Fulani 13 aka kama, inda aka samu gawar shiga daga cikin yayin da bakwai kuma ba a san inda suke ba har yanzu.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Daga ranar Lahadi 23 ga watan Yuli zuwa ranar Lahadi 31 ga watan Yuli mun binne mutum shida. Dukkanin wadanda aka kashe ba su san hawa ko sauka ba. Sannan har yanzu hudu kuma sun bace.

“Biyu daga cikin wadanda aka kashe sun fito ne daga Mongi sai kuma hudu ‘yan kauyen Langai. Daga cikin cikin wadanda aka kashe ya kammala jami’a sai kuma a cikinsu akwai dan shekara 65 dukka an kashe ba tare sun yi laifin komai ba.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“Wannan ba abu ne da za a lamunta ba. Ta’addanci ne marar dadi. Daukan hukuncin kisa lallai ba abu ne da ya kamata jama’a suke yi ba. Idan ana zarginsu da laifin garkuwa da mutane, kamata ya yi a kaisu kotu ta bincika ta hukuntasu ba wai wadanda suka kama su din su zartar musu kawai da hukuncin kisa ba.

“Ya kamata ne kotu ta bincika ta tabbatar da abun da ake zarginsu kafin a kai ga yanke musu hukunci.

“Bayan da aka kashe, wadanda suka kashe su din sun sace musu kadarorinsu da kudadensu. Sun kwashe musu Mashina. Muna kira ga hukumomin tsaro da su dauki mataki kan wannan lamarin. Na kuma sanar da GOC 3 Division kan wannan batun.”

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi, SP Ahmed Mohammed Wakil, ya ce rundunar su tana sane da faruwar lamarin sai dai kisan ya faru ne ba a karkashin ikonsu ba.

Ya ce, “Ban san cikakken abun da ya faru ba. Ina tunanin rundunar ‘yan sandan reshen jihar Filato ne suke da alhakin yin magana kan abun da ya faru.

“Ba mu da masaniya kan kungiyar da suke zargi. Idan sun san mutunan da suka kashe musu mambobi su nuna mana su. Don an ajiye gawarwakin wadanda aka kashe a Bauchi ba shine yake nufin an kashe a Bauchi ba ne.”

Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Da Dumi-Dumi: ASUU Ta Tsawaita Yajin Aikinta Zuwa Makonni 4

Da Dumi-Dumi: ASUU Ta Tsawaita Yajin Aikinta Zuwa Makonni 4

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.