ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe Makiyaya 6, Wasu Sun Bace Bat A Filato

by Khalid Idris Doya
4 years ago

Wasu makiyaya guda shida sun rigamu zuwa gidan gaskiya a yayin da wasu karin bakwai suka bace bat a kauyukan Mongi da Langai da ke karamar hukumar Mangu a jihar Filato.

Shugaban kungiyar Fulani (MACBAN) a jihar Filato, Malam Nura Abdullahi shi ne ya tabbatar da hakan, ya yi zargin cewa wasu mambobin kungiyar ‘yan banga da ke Bauchi ne a ranar 22 ga watan Yulin 2022 suka shiga cikin kauyukan tare da kama Fulanin hadi da kai su daji da kashe su.

  • Matsin Rayuwa: Za A Rage Farashin Man Fetur A Afrika Ta Kudu
  • NDLEA Ta Kwace Tiramol Miliyan 2.7 A Legas

Shugaban na MACBAN ya kara da cewa mambobinsu Fulani 13 aka kama, inda aka samu gawar shiga daga cikin yayin da bakwai kuma ba a san inda suke ba har yanzu.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Daga ranar Lahadi 23 ga watan Yuli zuwa ranar Lahadi 31 ga watan Yuli mun binne mutum shida. Dukkanin wadanda aka kashe ba su san hawa ko sauka ba. Sannan har yanzu hudu kuma sun bace.

“Biyu daga cikin wadanda aka kashe sun fito ne daga Mongi sai kuma hudu ‘yan kauyen Langai. Daga cikin cikin wadanda aka kashe ya kammala jami’a sai kuma a cikinsu akwai dan shekara 65 dukka an kashe ba tare sun yi laifin komai ba.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

“Wannan ba abu ne da za a lamunta ba. Ta’addanci ne marar dadi. Daukan hukuncin kisa lallai ba abu ne da ya kamata jama’a suke yi ba. Idan ana zarginsu da laifin garkuwa da mutane, kamata ya yi a kaisu kotu ta bincika ta hukuntasu ba wai wadanda suka kama su din su zartar musu kawai da hukuncin kisa ba.

“Ya kamata ne kotu ta bincika ta tabbatar da abun da ake zarginsu kafin a kai ga yanke musu hukunci.

“Bayan da aka kashe, wadanda suka kashe su din sun sace musu kadarorinsu da kudadensu. Sun kwashe musu Mashina. Muna kira ga hukumomin tsaro da su dauki mataki kan wannan lamarin. Na kuma sanar da GOC 3 Division kan wannan batun.”

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi, SP Ahmed Mohammed Wakil, ya ce rundunar su tana sane da faruwar lamarin sai dai kisan ya faru ne ba a karkashin ikonsu ba.

Ya ce, “Ban san cikakken abun da ya faru ba. Ina tunanin rundunar ‘yan sandan reshen jihar Filato ne suke da alhakin yin magana kan abun da ya faru.

“Ba mu da masaniya kan kungiyar da suke zargi. Idan sun san mutunan da suka kashe musu mambobi su nuna mana su. Don an ajiye gawarwakin wadanda aka kashe a Bauchi ba shine yake nufin an kashe a Bauchi ba ne.”

Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Next Post
Da Dumi-Dumi: ASUU Ta Tsawaita Yajin Aikinta Zuwa Makonni 4

Da Dumi-Dumi: ASUU Ta Tsawaita Yajin Aikinta Zuwa Makonni 4

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.