• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Nada Ibrahim Rilwan A Matsayin Sabon Garkuwan Matasan Arewa

by Sulaiman and Shehu Yahaya
1 year ago
in Labarai
0
An Nada Ibrahim Rilwan A Matsayin Sabon Garkuwan Matasan Arewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kao

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

Kungiyar Dalibban Nijeriya da hadin gwiwar kungiyar Matasan Arewa sun karrama Malam Ibrahim Rilwan Mohammed (Shugaban Gidauniyar IRM) a Matsayin Garkuwan Matasan Arewa.

Taron Wanda ya gudana a dakin taro na gidan Tarihi ( Arewa House) da ke Kaduna, kungiyar ta bukaci masu Hannu da shuni da su rika taimakawa marasa galihu a cikin al’umma.

  • Harin Gwoza: Gwamnonin Arewa Sun Bukaci Dakile ‘Yan Ta’adda Duk Inda Suke
  • Lamunin Naira Biliyan 5 Ga ‘Yan Fim: Yaushe Kannywood Za Ta Samu Nata?

A jawabinsa Mataimakin Shugaban Majalisar dalibban Nijeriya ( NANS) Kwamared Kabiru Aminu ya bayyana cewa an zabi wanda za a karramawar ne saboda dimbin gudumuwarsa ga ci gaban dalibban da kuma matasan Nijeriya a kowanne mataki. Bugu da kari ya bayyana namijin kokarin wanda aka karrama wajen sha’anin kyautata rayuwar mata da matasa ta hanyar sana’o’in hannu domin su kasance masu dogaro ga kawunan su a cikin garuruwan su, yana mai cewa irin kyakkyawar rawar da gidauniyar sa take takawa wajen daukaka Kalmar Allah ta hanyar ginin Masallatan Jumma’a da na Hamsar Sallawati da kuma Makarantun Islamiyya a birane da karkara a kowanne yankin dake cikin kasarnan da kuma Nijar.
Ya bayyana Malam Ibrahim Rilwan Mohammed a matsayin mai tsoron Allah da gudun duniya kari ga karimcinsa musamman ga marasa galihu.

A nasa jawabin Shugaban kungiyar Matasan Arewa (Arewa Youth Forum for Liberty) Abdulmalik Zakari ya bayyana cewa kungiyar tayi bincike mai zurfi wajen tantace mutane masu kokari da dawainiyar mutane ba tare da gajiyawa ba.
Ya kara da cewa samun irinsa ya yi wuya a yankin Arewa balle kuma a kasar bakidaya. Ya bayyana cewa Lambar Yabon da Sarautar Garkuwan Matasan Arewa za su karfafa masa gwiwa domin ya ci gaba da aiwatar da ayyukan alheri domin wasu su yi koyi dashi.
A cikin jawabinsa wani malamin Addinin Musulunci Farfesa Mansur Yalwa ya shawarci sabon Garkuwan Matasan Arewa da ya ci gaba da gudanar da ayyukan alheri domin Allah ba domin fadanci ba. Ya yabawa wadanda suka shirya taron saboda karrama mutane irin su Malam Ibrahim Rilwan Mohammed da su ke bayar da babbar gudumuwa wajen daukaka Kalmar Allah musamman abinda ya shafi sha’anin Ilimin Addinin Musulunci da Ilimin Zamani a kowanne mataki.
Da yake jawabi Shugaban Gidauniyar IRM kuma sabon Garkuwan Matasan Arewa Malam Ibrahim Rilwan Mohammed ya bayyana godiyarsa ga Kungiyar dalibban Nijeriya da kungiyar Matasan Arewa da suka zabe shi domin bashi Lambar Yabo da Sarautar Garkuwan Matasan Arewa. Ya bayyana cewa a matsayin sa na Musulmi ya yi daidai ya taimakawa mutane saboda yana daya daga cikin koyarwar Musulunci, ya bayyana cewa saboda haka yake taimako saboda Allah.
Ya bayyana cewa a shigo wani lokaci da mutane ba su taimakon makota KO ‘yan uwan su, kuma idan an ga wani na taimakon al’umma sai a danganta haka da cewa yana son wani mukamin siyasa ne. “Ina tabbata maku cewa ba domin siyasa ko son wani mukamin siyasa nake yin wannan taimako ba”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: iRMNANS
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jagororin Siyasar Arewa Raunana Ne Kuma A Rarrabe Suke – Salihu Lukman

Next Post

An Fara Kashe Kudi A Firimiyar Ingila

Related

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kao
Manyan Labarai

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kao

42 minutes ago
Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

11 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

11 hours ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

14 hours ago
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya
Ra'ayi Riga

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

17 hours ago
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas
Labarai

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

19 hours ago
Next Post
An Fara Kashe Kudi A Firimiyar Ingila

An Fara Kashe Kudi A Firimiyar Ingila

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kao

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kao

August 25, 2025
Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

August 25, 2025

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.