• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Nada Ibrahim Rilwan A Matsayin Sabon Garkuwan Matasan Arewa

by Sulaiman and Shehu Yahaya
10 months ago
in Labarai
0
An Nada Ibrahim Rilwan A Matsayin Sabon Garkuwan Matasan Arewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Kungiyar Dalibban Nijeriya da hadin gwiwar kungiyar Matasan Arewa sun karrama Malam Ibrahim Rilwan Mohammed (Shugaban Gidauniyar IRM) a Matsayin Garkuwan Matasan Arewa.

Taron Wanda ya gudana a dakin taro na gidan Tarihi ( Arewa House) da ke Kaduna, kungiyar ta bukaci masu Hannu da shuni da su rika taimakawa marasa galihu a cikin al’umma.

  • Harin Gwoza: Gwamnonin Arewa Sun Bukaci Dakile ‘Yan Ta’adda Duk Inda Suke
  • Lamunin Naira Biliyan 5 Ga ‘Yan Fim: Yaushe Kannywood Za Ta Samu Nata?

A jawabinsa Mataimakin Shugaban Majalisar dalibban Nijeriya ( NANS) Kwamared Kabiru Aminu ya bayyana cewa an zabi wanda za a karramawar ne saboda dimbin gudumuwarsa ga ci gaban dalibban da kuma matasan Nijeriya a kowanne mataki. Bugu da kari ya bayyana namijin kokarin wanda aka karrama wajen sha’anin kyautata rayuwar mata da matasa ta hanyar sana’o’in hannu domin su kasance masu dogaro ga kawunan su a cikin garuruwan su, yana mai cewa irin kyakkyawar rawar da gidauniyar sa take takawa wajen daukaka Kalmar Allah ta hanyar ginin Masallatan Jumma’a da na Hamsar Sallawati da kuma Makarantun Islamiyya a birane da karkara a kowanne yankin dake cikin kasarnan da kuma Nijar.
Ya bayyana Malam Ibrahim Rilwan Mohammed a matsayin mai tsoron Allah da gudun duniya kari ga karimcinsa musamman ga marasa galihu.

A nasa jawabin Shugaban kungiyar Matasan Arewa (Arewa Youth Forum for Liberty) Abdulmalik Zakari ya bayyana cewa kungiyar tayi bincike mai zurfi wajen tantace mutane masu kokari da dawainiyar mutane ba tare da gajiyawa ba.
Ya kara da cewa samun irinsa ya yi wuya a yankin Arewa balle kuma a kasar bakidaya. Ya bayyana cewa Lambar Yabon da Sarautar Garkuwan Matasan Arewa za su karfafa masa gwiwa domin ya ci gaba da aiwatar da ayyukan alheri domin wasu su yi koyi dashi.
A cikin jawabinsa wani malamin Addinin Musulunci Farfesa Mansur Yalwa ya shawarci sabon Garkuwan Matasan Arewa da ya ci gaba da gudanar da ayyukan alheri domin Allah ba domin fadanci ba. Ya yabawa wadanda suka shirya taron saboda karrama mutane irin su Malam Ibrahim Rilwan Mohammed da su ke bayar da babbar gudumuwa wajen daukaka Kalmar Allah musamman abinda ya shafi sha’anin Ilimin Addinin Musulunci da Ilimin Zamani a kowanne mataki.
Da yake jawabi Shugaban Gidauniyar IRM kuma sabon Garkuwan Matasan Arewa Malam Ibrahim Rilwan Mohammed ya bayyana godiyarsa ga Kungiyar dalibban Nijeriya da kungiyar Matasan Arewa da suka zabe shi domin bashi Lambar Yabo da Sarautar Garkuwan Matasan Arewa. Ya bayyana cewa a matsayin sa na Musulmi ya yi daidai ya taimakawa mutane saboda yana daya daga cikin koyarwar Musulunci, ya bayyana cewa saboda haka yake taimako saboda Allah.
Ya bayyana cewa a shigo wani lokaci da mutane ba su taimakon makota KO ‘yan uwan su, kuma idan an ga wani na taimakon al’umma sai a danganta haka da cewa yana son wani mukamin siyasa ne. “Ina tabbata maku cewa ba domin siyasa ko son wani mukamin siyasa nake yin wannan taimako ba”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: iRMNANS
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jagororin Siyasar Arewa Raunana Ne Kuma A Rarrabe Suke – Salihu Lukman

Next Post

An Fara Kashe Kudi A Firimiyar Ingila

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

8 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

9 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

10 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

12 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

13 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: TangarÉ—ar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

14 hours ago
Next Post
An Fara Kashe Kudi A Firimiyar Ingila

An Fara Kashe Kudi A Firimiyar Ingila

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: TangarÉ—ar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.