ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Fara Kashe Kudi A Firimiyar Ingila

by Sulaiman and Abubakar Sulaiman
2 years ago
Ingila

Kawo yanzu dai tuni kungiyoyin Premier League suka kashe kudi da yawa a kwana hudu a bana, an yi cinikin Fam miliyan 210.5 fiye da abin da aka kashe a watan Janairun wannan shekarar.

Kungiyoyi da yawa sun yi ciniki tun kafin ranar Lahadi, inda ranar Litinin aka sanar da wadanda aka dauka da wadanda aka sayar da kuma wadanda kungiyoyinsu ba za su kara musu sabon kwantiragi ba.

  • Yadda Rangers Ta Lashe Gasar Firimiyar Nijeriya 
  • Yadda Aka Kafa Tarihi A Gasar Firimiyar Ingila Da Aka Kammala

To amma kungiyoyin sun yi kokarin kauce wa debe musu maki, idan ba su kashe kudi daidai samu ba, wa’adin da ya cika ranar 30 ga watan Yuni kamar yadda hukumar kula da gasar firimiya ta tsara.

ADVERTISEMENT

Sai a ranar Juma’a 30 ga Agustan 2024 za a rufe kasuwar saye da sayar da ‘yan kwallo, tuni kuma kungiyoyin suka tsara yin cefanen ‘yan wasa da wuri kamar yadda aka saba duk shekara.

Kungiyoyin da suka fi yin cefane tun daga ranar 14 ga watan Yuni da aka bude kasuwar saye da sayar da ‘yan kwallo, sun hada da Aston Billa da Eberton da Chelsea da kuma Newcastle United.

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Aston Billa ta sanar da faduwa a kasuwanci na Fam miliyan 119m tun daga 31 ga watan Mayun, 2023, hakan ya sa ta cefanar da wasu ‘yan wasa don kar ta karya ka’ida kuma ta fuskanci fushin hukuma.

An kwashe maki shida a Eberton a kakar da ta wuce, bayan karya doka da ta yi har karo biyu, yayin da Chelsea ta kashe Fam biliyan daya tun bayan da Todd Boehly ya mallaki kungiyar a shekarar 2023.

Yawancin cinikin Chelsea kan kwantiragin kaka shida ta dunga yi, wadda ta dunga raba yadda take biya kudin da ta sayi dan wasa, hakan ya sa ba ta karya dokar kashe kudi daidai samu ba.

Wasu rahotannin sun ce Newcastle ta haura da Fam miliyan 50 na ka’ida a ranar Asabar da safe, hakan ya sa ta dauki mataki kafin a same ta da laifin da za a kwashe mata maki.

Ingila
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
  • Sulaiman
    Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
  • Sulaiman
    Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola
Ingila
Abubakar Sulaiman
Website |  + posts Bio
  • Abubakar Sulaiman
    Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé
  • Abubakar Sulaiman
    Real Madrid Ta Kammala Ɗaukar Bernardo Silva Daga Man City
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Ɗaure Mutane 5 Kan Tallafa Wa Boko Haram

MASU ALAKA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé
Wasanni

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?
Wasanni

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Real Madrid Ta Kammala Ɗaukar Bernardo Silva Daga Man City
Wasanni

Real Madrid Ta Kammala Ɗaukar Bernardo Silva Daga Man City

June 12, 2026
Next Post
Tsakanin Soyayyar Da Mace Ta Nema Da Wadda Namiji Ya Nema, Wacce Ta Fi Karko?

Tsakanin Soyayyar Da Mace Ta Nema Da Wadda Namiji Ya Nema, Wacce Ta Fi Karko?

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.