• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Nada Sanatan PDP Cikin Kwamitin Yakin Zaben Tinubu

Sunan Mataimakin Shugaban Kasa Ya Yi Batan-dabo Cikin Kwamitin

by Khalid Idris Doya
3 years ago
PDP

An nada mamba kuma jigo a jam’iyyar PDP sannan Sanatan da ke wakiltar mazabar Enugu ta Gabas, Chimaroke Nnamani a cikin kwamitin yakin zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC a zaben 2023 da ke karatowa.

Hakan na kunshe cikin jerin sunayen da aka fitar a daren ranar Juma’a inda aka nemi sunan mataimain shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo sama da kasa cikin jerin kwamitin yakin zaben na Tinubu aka rasa, inda aka rawaito cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari ne ya umarci mataimakin nasa da ya maida hankali kawai wajen gudanar da mulki.

  • Ministan Wajen Kasar Sin Ya Halarci Taron Ministocin BRICS
  • Dakarun Kasar Sin Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Wanzar Da Zaman Lafiya

Kazalika, jam’iyyar ta ki sanya sunan tsohon kakakin majalisar dokokin tarayya, Yakubu Dogara, tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir Lawal; tsohon ministan ilimi, Chukwuemeka Nwajiuba da dan-gani-kashenin Tinubu, Adebayo Shittu, wadda ya jagoranci manyan kungiyoyin goyon bayan Tinunu, ‘Asiwaju Tinubu-Shettima Coalition for Good Governance’ dukka babu sunayensu.

A wata sanarwar da jami’in watsa labarai na kwamitin yakin neman zaben Tinubu/Shettima, Festus Keyamo (SAN) ya fitar, ya ce an cire sunan Osianbajo da sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha daga cikin kwamitin yakin zaben ne sakamakon umarnin da shugaba Buhari ya bayar na cewa su maida hankali wajen gudanar da harkokin mulkin Nijeriya a halin yanzu.

Jerin kwamitin yakin zaben mai mutum 422 da sakataren kwamitin yakin zaben, Hon. James Faleke ya fitar, kuma an gano cewa wasu jerin fitattun jigogin jam’iyyar babu sunayensu a ciki.

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kazalika, shugaba Muhammadu Buhari shine shugaban kwamitin yakin zaben, Bola Ahmed Tinubu kuma shine mataimakin shugaba na kwamitin yakin zaben APC, yayin da kuma gwamnan jihar Filato, Simon Bako Lalong ya kasance darakta-janar yakin neman zabe na Tinubu.

Tsohon shugaban jam’iyyar, Kwamared Adams Oshiomhole shine aka ayyana a matsayin mataimakin darakta-janar nay akin zaben a sashin ayyuka, sanna akwai sunayen gwamnoni, ministoci, ‘yan majalisu, jakadu, da wasu jiga-jigai cikin kwamitin yakin zaben na Tinubu.

A sanarwar ta Keyamo, ya ce sabanin yadda wasu rahotonni ke yawo na cewa an cire sunayen wasu na kusa-kusan Buhari cikin kwamitin yakin zaben da kokarin nuna cewa akwai Baraka a jam’iyyar, ya ce sam ba haka zancen yake ba, illa dai ya nuna cewa Buhari ne ya umarci Osinbajo da Boss da su maida hankali wajen gudanar da mulki.

“A matsayin jam’iyyar da ta san meye take yi da gwamnatin da ta san meye take yi, ba zai yiyu a kwashe dukkanun manyan jami’an gwamnati a ce su bar ayyukansu su shiga kwamitin yakin zabe ba. APC ita ce ke da ikon jan ragamar Nijeriya har zuwa ranar 29 ga watan Mayun 2023, don haka akwai bukatar wasu su fi maida hankali wajen gudanar da harkokin mulki ba zallar yakin zabe ba.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kano
Manyan Labarai

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

November 3, 2025
Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba
Manyan Labarai

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Next Post
Wakilin Kasar Sin Ya Nuna Adawa Game Da Tsoma Baki Cikin Harkokin Gidan Burundi Ta Fakewa Da Kare Hakkin Dan Adam

Wakilin Kasar Sin Ya Nuna Adawa Game Da Tsoma Baki Cikin Harkokin Gidan Burundi Ta Fakewa Da Kare Hakkin Dan Adam

LABARAI MASU NASABA

Kano

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

November 3, 2025
Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.