ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Rantsar Da Sabbin Shugabannin Kananan Hukumomi A Adamawa

by Sulaiman and Muh'd Shafi'u Saleh
1 year ago
Adamawa

Babbar Alkalin Alkalan Jihar Adamawa, Mai Shari’a Hafsat Abdulrahman, ta rantsar da sabbin shugabannin kananan hukumomin jihar 21, a ranar Litinin 15 ga watan Yuli, 2024.

Hakan ya biyo bayan zaben da hukumar zabe ta jihar (ADSIEC) ta gudanar a ranar Asabar 13 ga watan Yuli, inda jam’iyyar PDP ta lashe dukkan kujerun shugabannin 21 da na kansiloli 225 yayin da jam’iyyar NNPP, ta samu kujerar kansila daya a karamar hukumar Demsa.

  • Da Ɗumi-ɗumi: An Ɗagewa Nijeriya Takunkumi Kan Tafiya Zuwa Dubai
  • Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Kaduna

Da yake jawabi a taron gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, ya kalubalanci shugabannin da su guji hanci da cin rashawa tare da rungumar kowa da kowa a gwamnatinsu.

ADVERTISEMENT

Gwamnan ya kuma gargadi sabbin shugabannin da kansiloli da su guji rashin zuwa aiki akan lokaci, domin gwamnati mai ci ba za ta lamunci irin wannan dabi’a ta yadda shugaba zai yi watsi da aikinsa ba tare da wani dalili ba.

Gwamna Umaru Fintiri ya jinjinawa hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar ADSIEC bisa gudanar da zaben da aka amince da shi a matsayin wanda ya fi kowanne inganci a tarihin jihar Adamawa.

LABARAI MASU NASABA

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

Haka kuma gwamnan ya taya shuwagabannin jam’iyyar PDP da shugabannin murnar nasarar da suka samu a lokacin zaben, ya bukaci jama’a da su ci gaba da kasancewa masu biyayya da goyon baya ga gwamnatinsa domin ci gaban al’ummar jihar.

Shugaban jam’iyyar PDP na jihar Barista A T Shehu a jawabinsa, ya tunatar da shugabannin da aka rantsar cewa an zabe su ne bisa mutuncin gwamna Umaru Fintiri, inda ya bukace su da su yi koyi da shi tare da samar da shugabanci na gari.

A jawabin godiya a madadin takwarorinsa, Suleiman Ahmed, sabon shugaban karamar hukumar Toungo, ya ce wa’adin da suke dashi na shekara biyu, ba zai wadatar ba muddin ba tare da kyakkyawan shugabancin gwamna Fintiri ya shimfida ba.

Ya kuma jaddada aniyarsu na gudanar da ayyukansu da kuma aiki bisa tsarin ci gaban wannan gwamnati mai ci domin amfanin al’ummar Adamawa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026
Labarai

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano
Kotu Da Ɗansanda

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026
Labarai

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Next Post
Sin Ta Fadada Manufar Yada Zango A Kasar Ba Tare Da Biza Ba Zuwa Karin Tashoshi

Sin Ta Fadada Manufar Yada Zango A Kasar Ba Tare Da Biza Ba Zuwa Karin Tashoshi

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.