• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Rantsar Da Sabbin Shugabannin Kananan Hukumomi A Adamawa

by Sulaiman and Muh'd Shafi'u Saleh
11 months ago
in Labarai
0
An Rantsar Da Sabbin Shugabannin Kananan Hukumomi A Adamawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babbar Alkalin Alkalan Jihar Adamawa, Mai Shari’a Hafsat Abdulrahman, ta rantsar da sabbin shugabannin kananan hukumomin jihar 21, a ranar Litinin 15 ga watan Yuli, 2024.

Hakan ya biyo bayan zaben da hukumar zabe ta jihar (ADSIEC) ta gudanar a ranar Asabar 13 ga watan Yuli, inda jam’iyyar PDP ta lashe dukkan kujerun shugabannin 21 da na kansiloli 225 yayin da jam’iyyar NNPP, ta samu kujerar kansila daya a karamar hukumar Demsa.

  • Da Ɗumi-ɗumi: An Ɗagewa Nijeriya Takunkumi Kan Tafiya Zuwa Dubai
  • Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Kaduna

Da yake jawabi a taron gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, ya kalubalanci shugabannin da su guji hanci da cin rashawa tare da rungumar kowa da kowa a gwamnatinsu.

Gwamnan ya kuma gargadi sabbin shugabannin da kansiloli da su guji rashin zuwa aiki akan lokaci, domin gwamnati mai ci ba za ta lamunci irin wannan dabi’a ta yadda shugaba zai yi watsi da aikinsa ba tare da wani dalili ba.

Gwamna Umaru Fintiri ya jinjinawa hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar ADSIEC bisa gudanar da zaben da aka amince da shi a matsayin wanda ya fi kowanne inganci a tarihin jihar Adamawa.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Haka kuma gwamnan ya taya shuwagabannin jam’iyyar PDP da shugabannin murnar nasarar da suka samu a lokacin zaben, ya bukaci jama’a da su ci gaba da kasancewa masu biyayya da goyon baya ga gwamnatinsa domin ci gaban al’ummar jihar.

Shugaban jam’iyyar PDP na jihar Barista A T Shehu a jawabinsa, ya tunatar da shugabannin da aka rantsar cewa an zabe su ne bisa mutuncin gwamna Umaru Fintiri, inda ya bukace su da su yi koyi da shi tare da samar da shugabanci na gari.

A jawabin godiya a madadin takwarorinsa, Suleiman Ahmed, sabon shugaban karamar hukumar Toungo, ya ce wa’adin da suke dashi na shekara biyu, ba zai wadatar ba muddin ba tare da kyakkyawan shugabancin gwamna Fintiri ya shimfida ba.

Ya kuma jaddada aniyarsu na gudanar da ayyukansu da kuma aiki bisa tsarin ci gaban wannan gwamnati mai ci domin amfanin al’ummar Adamawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bukaci WTO Ta Samar Da Majalisar Kwararru Masu Shiga Tsakani Game Da Takaddama Da Amurka Game Da EVs Masu Rangwame

Next Post

Sin Ta Fadada Manufar Yada Zango A Kasar Ba Tare Da Biza Ba Zuwa Karin Tashoshi

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

5 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

6 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

7 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

11 hours ago
Adamawa
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

12 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

13 hours ago
Next Post
Sin Ta Fadada Manufar Yada Zango A Kasar Ba Tare Da Biza Ba Zuwa Karin Tashoshi

Sin Ta Fadada Manufar Yada Zango A Kasar Ba Tare Da Biza Ba Zuwa Karin Tashoshi

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.