ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

by Khalid Idris Doya
8 months ago
Gombe

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, ya gabatar da ƙudurin kasafin kuɗin 2026 na Naira biliyan 535,691,983 ga majalisar dokokin Jihar Gombe domin amincewa da shi.

Da yake gabatar da ƙudurin kasafin kuɗin a gaban ‘yan majalisan a ranar Alhamis, Gwamna Inuwa ya bayyana cewa an ware Naira biliyan 164.25 a matsayin kasafin gudanarwa na yau da kullum.

  • Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani
  • Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

An kuma ware Naira biliyan 371.44 don gudanar da manyan ayyuka.

ADVERTISEMENT

Kasafin kuɗin, wadda aka yi wa laƙabi da “kasafin bunƙasa ayyukan ci gaba,” an tsara shi ne don ƙarfafa nasarorin da aka samu a baya-bayan nan da tabbatar da ɗorewar ci gaban rayuwar al’ummar jihar.

Gwamna Yahaya ya ce kasafin kuɗin na 2026 za a aiwatar da shi ne ta hanyoyin samun kuɗaɗen shiga da suka haɗa da harajin da ake samu a cikin gida, da kason da ke zuwa daga gwamnatin tarayya, da na harajin VAT da sauran kuɗaɗen da ke zuwa daga asusun haɗaka na tarayya (FAAC).

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Da yake ƙarin haske kan muhimman sassan da aka fi bai wa fifiko, Gwamnan ya bayyana cewa, ɓangaren tattalin arziƙi da ci gaban al’umma ne suka samu kaso mafi tsoka na kasafin kuɗin, inda aka ware sama da Naira biliyan 269 don sanya hannun jari a muhimman fannoni.

Fannin ayyuka, gidaje da sufuri ne ke kan gaba da Naira Biliyan 135.9, sai ruwa, muhalli da gandun daji da aka warewa Naira Biliyan 88.4, yayin da noma, kiwo da ƙungiyoyin gama ya samu Naira biliyan 20.57.

A fannin harkokin zamantakewa, an ware Naira biliyan 80 don samar da ayyukan ci gaba da gina jama’a, inda ilimi ya samu Naira biliyan 31.9, yayinda ilimi mai zurfi ya samu Naira biliyan 17.5.

Ɓangaren kiwon lafiya ya samu Naira biliyan 25.9, wanda hakan ke nuna yadda gwamnati ke ci gaba da zuba jari wajen samar da lafiya mai inganci.

Fannin gudanarwa ya samu Naira biliyan 19.63, sannan ɓangaren doka da shari’a aka ware masa Naira biliyan 2.17, fannin filaye ya samu Naira biliyan 6.46; shi kuwa fannin Kasuwanci, Masana’antu da Yawon Buɗe Ido ya samu Naira biliyan 4.02.

Yayin da sashen matasa da ci gaban wasanni ya samu Naira biliyan 3.33; harkokin mata da ci gaban a’umma Naira biliyan 1.28; fannin yaɗa Labarai da raya al’adu kuwa Naira biliyan 10.38.

Gwamna Yahaya ya bayyana ƙididdigar kasafin kuɗin na 2026 a matsayin na ɗorawa kan ci gaban da gwamnatinsa ta faro na gudanar da shugabanci nagari, Gwamna Inuwa Yahaya ya yi ƙira ga majalisar akan ta yi nazari tare da ƙalailaice ƙudurin tare da sanya gudunmawa da tabarrukinta.

“Aikin dake gabanmu shi ne mu samarwa al’ummarmu kasafin kuɗin da zai wanzar da fatansu ya zuwa zahiri da kuma kyautata makomarsu,” in ji shi.

Kasafin kuɗin na 2026 ya dace da tsarin ci gaban Jihar Gombe (DEVAGOM) da kuma tsarin tattalin arziƙin ƙasa baki ɗaya. Da yake tsokaci kan harkokin tattalin arziƙi a dunƙule, Gwamnan ya ce sauye-sauyen da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ɓullo da su, da suka haɗa da cire tallafin man fetur da sakin mara ga canjin kuɗaɗen waje, sun fara haifar da sakamako na ƙwarai.

A nasa jawabin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Gombe Rt. Hon. Muhammad Abubakar Luggerewo, ya yabawa Gwamna Inuwa Yahaya bisa yadda gwamnatinsa ta himmatu wajen tabbatar da bin doka da oda, da gaskiya da kuma tsantseni wajen tafiyar da harkokin kuɗaɗen gwamnati.

Ya bada tabbacin duba kasafin akan lokaci da kuma gaggauta amincewa da ƙudurin kasafin na 2026.

Rt. Hon. Luggerewo ya kuma nuna jin daɗinsa da yadda jihar ke tafiyar da harkokin kasafin kuɗi, inda ya ce aiwatar da kasafin kuɗin 2025 ya samu nasarar fiye da kaso 60 cikin 100 ya zuwa ƙarshen watan Satumba, sannan ya yaba da yadda gwamnati ta samu ci gaba a fannin samar da ababen more rayuwa, kiwon lafiya, ilimi, masana’antu, da sabunta birane.

“Za mu ci gaba da tallafawa manufofi da tsare-tsaren dake tabbatar da zaman lafiya, inganta ci gaban tattalin arziki da kyautata rayuwar jama’armu,” in ji kakakin.

A shekarar da ake ciki ta 2025, Gwamnatin Inuwa ta yi kasafi ne na fiye da Naira biliyan 369.9, inda daga baya aka yi bitarsa ya koma na fiye da Naira biliyan 451.6 biyo bayan samun ƙarin kuɗaɗen shiga fiye da yadda aka yi tsammani.

Gombe
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
Next Post
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.