ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

by Muhammad
7 months ago
BUK

Majalisar Gudanarwa ta Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta amince da kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa, wadda za ta kasance cibiyar farko irinta da wata jami’a za ta kafa a Nijeriya.

An cimma wannan matsaya ne a taron Majalisar Zartarwar Jami’ar na 429, da aka gudanar a ranar Laraba, 29 ga Oktoba, 2025, a wani bangare na ƙoƙarin jami’ar na inganta ilimin aikin jarida da kuma tunkarar manyan sauye-sauyen da ke faruwa cikin sauri a fagen sadarwa.

  • Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya
  • Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Tuni an samar da kudaden da za a yi amfani da su wajen fara kafa cibiyar, wadda za ta mayar da hankali kan shirye-shiryen digiri na biyu da na uku, horaswar aiki ta zahiri, gudanar da bincike, da kuma haɓaka haɗin gwiwa da masana’antar kafofin watsa labarai. Babbar manufarta ita ce cike gibi tsakanin darussan da ake koyarwa a aji da kuma yadda ake aiwatar da su a wajen aiki, tare da tallafa wa ‘yan jarida da masu bincike su samu cikakken ilimi da kwarewar da ta dace da zamanin dijital.

ADVERTISEMENT

A cewar Majalisar Gudanarwar Jami’ar, kafa cibiyar na da alaƙa da fahimtar irin sauyin da kafafen watsa labarai na duniya ke yi da kuma bukatar zurfafa bincike a fannin aikin jarida, sababbin fasahohi, da labarai na dijital. Da zarar cibiyar ta fara aiki, ana sa ran za ta ƙara tabbatar da matsayin BUK a matsayin jagora a fannin ilimin jarida da sabbin kirkire-kirkire a Nijeriya.

Jami’ar ta bayyana wannan mataki a matsayin wani mahimmin ci gaba da ya yi daidai da manufarta ta bunƙasa bincike, haɓaka kirkira, da gina ƙwararrun masana.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

An fara koyar da aikin jarida a Nijeriya tun farkon bayan samun ‘yancin kai, kuma BUK ta kasance cikin jami’o’in farko da suka kafa sashen Koyar da Aikin Jarida (Mass Communication). A tsawon shekaru, jami’ar ta samar da fitattun ‘yan jarida, malamai, da ƙwararrun ma’aikatan kafofin watsa labarai da ke taka rawa a fadin ƙasar.

An gina ra’ayin kafa wannan cibiyar ne a ƙarƙashin jagorancin Farfesa Umaru A. Pate, shahararren masani a fannin jarida kuma jajirtaccen mai fafutukar gyaran tsarin kafafen yaɗa labarai a ƙasa. Hangen nesa da shawarwarinsa sun taka muhimmiyar rawa wajen zurfafa madogarar bincike da ci gaban ilimin jarida a BUK.

Da zarar an kammala cikakken kafuwar cibiyar, ana sa ran za ta ƙara ɗaukaka sunan Jami’ar Bayero Kano, tare da ƙarfafa matsayinta a matsayin cibiyar ƙwarewa, kirkira, da bin ka’idojin aikin jarida na gaskiya da rikon amana.

BUK
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
Labarai

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya
Rahotonni

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.