• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Samu Karin Yawan Hannun Jari A Aikin Noma Da Kashi 226 Cikin Wata Uku

by Abubakar Abba
8 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da kalubalen rashin tsaron da Nijeriya ke ci gaba da fuskanta, hukumar kididiga ta kasa (NBS) ta sanar da cewa, zuba hannun jari kai tsaye na kasashen kere a fannin aikin noma, ya karu da kashi 226.45 cikin watanni uku na 2024 a Nijeriya, musamman idan aka kwatanta da zango na 2023.

Rahoton baya na shigo da kaya cikin kasar na hukumar ya nuna cewa, zuba hannun jari na kai tsaye cikin fannin aikin noman a zango na daya na 2024, daga dala miliyan 4.84; yanzu ya kai dala miliyan 15.80 daidai da na zangon farko na 2023.

  • Wane Ne Ke Tallafa Wa Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Da Kudade?
  • Gidauniyar Buratai Ta Taya Giwa-Daramola Murnar Zama Shugaban Kungiyar Tseren Kwale-kwale Na Ondo

Haka zalika, daga zango zuwa zango; zuba hannun jari na kai tsaye, ya karu zuwa kashi 3,661.90 a zango na hudu na 2023, wanda ya kai dala miliyan 0.42.

Duk da matsalar ta rashin tsaro da ke hana manoma zuwa noma gonakinsu ta hanyar daukar hayar jam’in tsaro masu zaman kansu, zuba hannun jari na kai tsaye a fannin aikin noman kasar, ya karu matuka tun a zangon farko na 2022.

Wani masani a fannin aikin noma, Africanfarmer Mogaji; ya sanar da cewa, sakamakon gibin da ake da shi na samar da wadaccen abinci a kasar; wasu ‘yan kasashen waje na yin amfani da wannan dama wajen zuba hannun jarinsu a fannin, don samun riba mai yawa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

A cewarsa, “Mu ‘yan Nijeriya, mu ne muke ganin kaluabalen rashin tsaro, amma su ‘yan kasashen wajen na yin amfani da wannan damar suna zuba jarinsu a fannin”.

Ya kara da cewa, zuwa zango na gaba ‘yan ketaren za su kara yin amfani da wannan dama ta kalubalen rashin tsaro a kasar; ta yadda za su kara zuba hannun jarinsu a fannin da yawan gaske.

Ya ci gaba da cewa, a Nijeriya ba a tanadi ingantaccen tsari a fannin aikin noma ba, haka nan ba a kuma samar da kayan aikin noman ingantattu ba, musamman don cike gibin da ake da shi na samar da wadataccen abinci, wanda hakan ke ci gaba da bai wa ‘yan kasar waje damar zuba hannun harinsu a fannin aikin noma na kasar.

Kazalika, ya sanar da cewa; fannin ya taimaka wa tattalin arzikin kasar a zango na daya a 2024 daga kashi 0.18 ya kai har kashi 2.19 a lokaci guda a bara.

Shi ma wani masani a fannin, Ibrahim Tajuddeen ya sanar da cewa; gibin da aka samu da kuma kalubalen da ake ci gaba da fuskanta na rashin tsaro a kasar ne ya haifar da yawan samun ‘yan ketare, suna zuwa suna zuba hannun jarinsu a fannin aikin noman kasar.

A zango na daya na 2024, jimillar kudade na Nijeriya na shigo da kaya ya karu zuwa kashi 198.06, wanda aka kuma samu dala biliyan 1.13 a zango na daya na 2023 zuwa dala biliyan 3.37, duk a wannan lokaci.

An kuma samu karin da ya kai kashi 210.16 daga zango zuwa zango daga dala biliyan 1.08 a zango na hudu na 4 na rubi’in shekarar 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hannun JariNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bukaci Gwamnain Tarayya Ta Sake Inganta Harkokin Amfanin Gona

Next Post

Faransa Ta Shirya Bikin Baje Kolin Hanyoyin Bunƙasa Kasuwancin Kayan Abinci A Nijeriya

Related

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

6 days ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

6 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

6 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

2 weeks ago
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

3 weeks ago
Next Post
Faransa Ta Shirya Bikin Baje Kolin Hanyoyin Bunƙasa Kasuwancin Kayan Abinci A Nijeriya

Faransa Ta Shirya Bikin Baje Kolin Hanyoyin Bunƙasa Kasuwancin Kayan Abinci A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.