• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Samu Karin Yawan Hannun Jari A Aikin Noma Da Kashi 226 Cikin Wata Uku

by Abubakar Abba
12 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da kalubalen rashin tsaron da Nijeriya ke ci gaba da fuskanta, hukumar kididiga ta kasa (NBS) ta sanar da cewa, zuba hannun jari kai tsaye na kasashen kere a fannin aikin noma, ya karu da kashi 226.45 cikin watanni uku na 2024 a Nijeriya, musamman idan aka kwatanta da zango na 2023.

Rahoton baya na shigo da kaya cikin kasar na hukumar ya nuna cewa, zuba hannun jari na kai tsaye cikin fannin aikin noman a zango na daya na 2024, daga dala miliyan 4.84; yanzu ya kai dala miliyan 15.80 daidai da na zangon farko na 2023.

  • Wane Ne Ke Tallafa Wa Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Da Kudade?
  • Gidauniyar Buratai Ta Taya Giwa-Daramola Murnar Zama Shugaban Kungiyar Tseren Kwale-kwale Na Ondo

Haka zalika, daga zango zuwa zango; zuba hannun jari na kai tsaye, ya karu zuwa kashi 3,661.90 a zango na hudu na 2023, wanda ya kai dala miliyan 0.42.

Duk da matsalar ta rashin tsaro da ke hana manoma zuwa noma gonakinsu ta hanyar daukar hayar jam’in tsaro masu zaman kansu, zuba hannun jari na kai tsaye a fannin aikin noman kasar, ya karu matuka tun a zangon farko na 2022.

Wani masani a fannin aikin noma, Africanfarmer Mogaji; ya sanar da cewa, sakamakon gibin da ake da shi na samar da wadaccen abinci a kasar; wasu ‘yan kasashen waje na yin amfani da wannan dama wajen zuba hannun jarinsu a fannin, don samun riba mai yawa.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

A cewarsa, “Mu ‘yan Nijeriya, mu ne muke ganin kaluabalen rashin tsaro, amma su ‘yan kasashen wajen na yin amfani da wannan damar suna zuba jarinsu a fannin”.

Ya kara da cewa, zuwa zango na gaba ‘yan ketaren za su kara yin amfani da wannan dama ta kalubalen rashin tsaro a kasar; ta yadda za su kara zuba hannun jarinsu a fannin da yawan gaske.

Ya ci gaba da cewa, a Nijeriya ba a tanadi ingantaccen tsari a fannin aikin noma ba, haka nan ba a kuma samar da kayan aikin noman ingantattu ba, musamman don cike gibin da ake da shi na samar da wadataccen abinci, wanda hakan ke ci gaba da bai wa ‘yan kasar waje damar zuba hannun harinsu a fannin aikin noma na kasar.

Kazalika, ya sanar da cewa; fannin ya taimaka wa tattalin arzikin kasar a zango na daya a 2024 daga kashi 0.18 ya kai har kashi 2.19 a lokaci guda a bara.

Shi ma wani masani a fannin, Ibrahim Tajuddeen ya sanar da cewa; gibin da aka samu da kuma kalubalen da ake ci gaba da fuskanta na rashin tsaro a kasar ne ya haifar da yawan samun ‘yan ketare, suna zuwa suna zuba hannun jarinsu a fannin aikin noman kasar.

A zango na daya na 2024, jimillar kudade na Nijeriya na shigo da kaya ya karu zuwa kashi 198.06, wanda aka kuma samu dala biliyan 1.13 a zango na daya na 2023 zuwa dala biliyan 3.37, duk a wannan lokaci.

An kuma samu karin da ya kai kashi 210.16 daga zango zuwa zango daga dala biliyan 1.08 a zango na hudu na 4 na rubi’in shekarar 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hannun JariNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bukaci Gwamnain Tarayya Ta Sake Inganta Harkokin Amfanin Gona

Next Post

Faransa Ta Shirya Bikin Baje Kolin Hanyoyin Bunƙasa Kasuwancin Kayan Abinci A Nijeriya

Related

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

1 day ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

1 day ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

1 week ago
Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

1 week ago
Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona

1 week ago
Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

2 weeks ago
Next Post
Faransa Ta Shirya Bikin Baje Kolin Hanyoyin Bunƙasa Kasuwancin Kayan Abinci A Nijeriya

Faransa Ta Shirya Bikin Baje Kolin Hanyoyin Bunƙasa Kasuwancin Kayan Abinci A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.