ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Samu Karin Yawan Hannun Jari A Aikin Noma Da Kashi 226 Cikin Wata Uku

by Abubakar Abba
2 years ago
Hannun Jari

Duk da kalubalen rashin tsaron da Nijeriya ke ci gaba da fuskanta, hukumar kididiga ta kasa (NBS) ta sanar da cewa, zuba hannun jari kai tsaye na kasashen kere a fannin aikin noma, ya karu da kashi 226.45 cikin watanni uku na 2024 a Nijeriya, musamman idan aka kwatanta da zango na 2023.

Rahoton baya na shigo da kaya cikin kasar na hukumar ya nuna cewa, zuba hannun jari na kai tsaye cikin fannin aikin noman a zango na daya na 2024, daga dala miliyan 4.84; yanzu ya kai dala miliyan 15.80 daidai da na zangon farko na 2023.

  • Wane Ne Ke Tallafa Wa Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Da Kudade?
  • Gidauniyar Buratai Ta Taya Giwa-Daramola Murnar Zama Shugaban Kungiyar Tseren Kwale-kwale Na Ondo

Haka zalika, daga zango zuwa zango; zuba hannun jari na kai tsaye, ya karu zuwa kashi 3,661.90 a zango na hudu na 2023, wanda ya kai dala miliyan 0.42.

ADVERTISEMENT

Duk da matsalar ta rashin tsaro da ke hana manoma zuwa noma gonakinsu ta hanyar daukar hayar jam’in tsaro masu zaman kansu, zuba hannun jari na kai tsaye a fannin aikin noman kasar, ya karu matuka tun a zangon farko na 2022.

Wani masani a fannin aikin noma, Africanfarmer Mogaji; ya sanar da cewa, sakamakon gibin da ake da shi na samar da wadaccen abinci a kasar; wasu ‘yan kasashen waje na yin amfani da wannan dama wajen zuba hannun jarinsu a fannin, don samun riba mai yawa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

A cewarsa, “Mu ‘yan Nijeriya, mu ne muke ganin kaluabalen rashin tsaro, amma su ‘yan kasashen wajen na yin amfani da wannan damar suna zuba jarinsu a fannin”.

Ya kara da cewa, zuwa zango na gaba ‘yan ketaren za su kara yin amfani da wannan dama ta kalubalen rashin tsaro a kasar; ta yadda za su kara zuba hannun jarinsu a fannin da yawan gaske.

Ya ci gaba da cewa, a Nijeriya ba a tanadi ingantaccen tsari a fannin aikin noma ba, haka nan ba a kuma samar da kayan aikin noman ingantattu ba, musamman don cike gibin da ake da shi na samar da wadataccen abinci, wanda hakan ke ci gaba da bai wa ‘yan kasar waje damar zuba hannun harinsu a fannin aikin noma na kasar.

Kazalika, ya sanar da cewa; fannin ya taimaka wa tattalin arzikin kasar a zango na daya a 2024 daga kashi 0.18 ya kai har kashi 2.19 a lokaci guda a bara.

Shi ma wani masani a fannin, Ibrahim Tajuddeen ya sanar da cewa; gibin da aka samu da kuma kalubalen da ake ci gaba da fuskanta na rashin tsaro a kasar ne ya haifar da yawan samun ‘yan ketare, suna zuwa suna zuba hannun jarinsu a fannin aikin noman kasar.

A zango na daya na 2024, jimillar kudade na Nijeriya na shigo da kaya ya karu zuwa kashi 198.06, wanda aka kuma samu dala biliyan 1.13 a zango na daya na 2023 zuwa dala biliyan 3.37, duk a wannan lokaci.

An kuma samu karin da ya kai kashi 210.16 daga zango zuwa zango daga dala biliyan 1.08 a zango na hudu na 4 na rubi’in shekarar 2023.

Hannun Jari
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Faransa Ta Shirya Bikin Baje Kolin Hanyoyin Bunƙasa Kasuwancin Kayan Abinci A Nijeriya

Faransa Ta Shirya Bikin Baje Kolin Hanyoyin Bunƙasa Kasuwancin Kayan Abinci A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.