• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Shiga Alhinin Kisan Gillar Da Aka Yi Wa Sheikh Goni Aisami Gashuwa, A Yobe

by Muhammad Maitela
3 years ago
Kisan Gillar

Al’ummar Jihar Yobe sun na ci gaba da alhinin kisan gillar da aka yi wa Shehin Malamin addinin Musulunci, Sheikh Goni Aisami Gashuwa, wanda ake zargin wasu jami’an tsaro ne suka kashe shi.

Ana zargin sun kashe shi da misalin karfe 10:00 na daren ranar Juma’a, kan hanyarsa ta dawowa daga Kano zuwa Gashuwa.

  • Yanzu-Yanzu: SSANU Da NASU Sun Janye Yajin Aiki Bayan Ganawa Da Ministan Ilimi
  • Babu Wanda Zai Fice Daga NNPP Da Zai Girgiza Siyasar Kwankwaso – Kofa

Kamar yadda wata majiya daga bakin wani jami’in tsaro a garin Jaji-maji, shelkwatar karamar hukumar Karasuwa ya shaida wa LEADERSHIP Hausa cewa, maharan sun biyo shi ne a mota kirar Sharon, wanda suka tare motarsa bayan ya fita daga kauyen Chakama mai tazarar kilomita 3 zuwa garin Jaji-maji.

“Shi kadai ne a motar kuma da alama sun biyo shi ne ne bisa zaton yana dauke da kudi, a kan hanyarsa daga Kano zuwa gida. Wanda bayan sun harbe shi a ciki tare da soka masa wuka a jiki, sannan suka ja gawarsa zuwa gindin kaba. Kuma cikin ikon Allah basu bar inda gawarsa take ba har gari ya waye.”

“Ana haka sai ga jama’a masu tafiya gona, wanda nan take suka shaida wa Lawanin Jaji-maji, Lawan Manaja inda nan take ya nemi ‘yansanda da ke aiki a garin.” In ji majiyar.

LABARAI MASU NASABA

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Bugu da kari, majiyar tsaro a garin Jaji-maji ta bayyana cewa, “Ana zargin wasu sojoji biyu da kisan malamin, wanda kuma tuni ‘yansanda suka kama su tare da bindigogi biyu.

“Sannan zancen da nake da kai yanzu haka an garzaya dasu zuwa Damaturu, babban birnin Jihar Yobe don ci gaba da bincike,” a cewarsa.

A hannu guda kuma, wannan rashi na Sheikh Goni Aisami Gashuwa, ya tayar da hankulan al’ummar garin Gashuwa da Jihar Yobe baki daya, saboda kasancewarsa mutum mai kokari kuma Malami mai karantar da al’umma sama da shekaru 30 da suka gabata.

Mai magana da yawun rundunar ‘yansandan Jihar Yobe, ASP Dungus Abdulkarim, ya tabbatar wa da wakilinmu a jihar cewa, sun samu bayanin afkuwar lamarin tare da kokarin da jami’ansu a garin suka yi na kama wadanda ake zargi da aikata laifi.

Ya kara da cewa yanzu haka suka hannun jami’an tsaron binciken manyan laifuka (CID) a Damaturu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru
Wasanni

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL
Manyan Labarai

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
Next Post
Ana Samun Sakamako Mai Kyau A Hadin Gwiwar Dake Tsakanin Sin Da Afirka

Ana Samun Sakamako Mai Kyau A Hadin Gwiwar Dake Tsakanin Sin Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana’o’i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu

October 26, 2025
Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

October 26, 2025
Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.