• English
  • Business News
Thursday, September 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Shiga Alhinin Kisan Gillar Da Aka Yi Wa Sheikh Goni Aisami Gashuwa, A Yobe

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Manyan Labarai
0
An Shiga Alhinin Kisan Gillar Da Aka Yi Wa Sheikh Goni Aisami Gashuwa, A Yobe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Al’ummar Jihar Yobe sun na ci gaba da alhinin kisan gillar da aka yi wa Shehin Malamin addinin Musulunci, Sheikh Goni Aisami Gashuwa, wanda ake zargin wasu jami’an tsaro ne suka kashe shi.

Ana zargin sun kashe shi da misalin karfe 10:00 na daren ranar Juma’a, kan hanyarsa ta dawowa daga Kano zuwa Gashuwa.

  • Yanzu-Yanzu: SSANU Da NASU Sun Janye Yajin Aiki Bayan Ganawa Da Ministan Ilimi
  • Babu Wanda Zai Fice Daga NNPP Da Zai Girgiza Siyasar Kwankwaso – Kofa

Kamar yadda wata majiya daga bakin wani jami’in tsaro a garin Jaji-maji, shelkwatar karamar hukumar Karasuwa ya shaida wa LEADERSHIP Hausa cewa, maharan sun biyo shi ne a mota kirar Sharon, wanda suka tare motarsa bayan ya fita daga kauyen Chakama mai tazarar kilomita 3 zuwa garin Jaji-maji.

“Shi kadai ne a motar kuma da alama sun biyo shi ne ne bisa zaton yana dauke da kudi, a kan hanyarsa daga Kano zuwa gida. Wanda bayan sun harbe shi a ciki tare da soka masa wuka a jiki, sannan suka ja gawarsa zuwa gindin kaba. Kuma cikin ikon Allah basu bar inda gawarsa take ba har gari ya waye.”

“Ana haka sai ga jama’a masu tafiya gona, wanda nan take suka shaida wa Lawanin Jaji-maji, Lawan Manaja inda nan take ya nemi ‘yansanda da ke aiki a garin.” In ji majiyar.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Bayar Da Umarni Karya Farashin Kayan Abinci A Nijeriya

Mele Kyari Ya Bayyana A Ofishin EFCC Kan Zargin Badaƙalar Dala Biliyan 7.2

Bugu da kari, majiyar tsaro a garin Jaji-maji ta bayyana cewa, “Ana zargin wasu sojoji biyu da kisan malamin, wanda kuma tuni ‘yansanda suka kama su tare da bindigogi biyu.

“Sannan zancen da nake da kai yanzu haka an garzaya dasu zuwa Damaturu, babban birnin Jihar Yobe don ci gaba da bincike,” a cewarsa.

A hannu guda kuma, wannan rashi na Sheikh Goni Aisami Gashuwa, ya tayar da hankulan al’ummar garin Gashuwa da Jihar Yobe baki daya, saboda kasancewarsa mutum mai kokari kuma Malami mai karantar da al’umma sama da shekaru 30 da suka gabata.

Mai magana da yawun rundunar ‘yansandan Jihar Yobe, ASP Dungus Abdulkarim, ya tabbatar wa da wakilinmu a jihar cewa, sun samu bayanin afkuwar lamarin tare da kokarin da jami’ansu a garin suka yi na kama wadanda ake zargi da aikata laifi.

Ya kara da cewa yanzu haka suka hannun jami’an tsaron binciken manyan laifuka (CID) a Damaturu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaAlhiniJami'an TsaroKisan gillaSheikh Goni GashuwaYobe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yanzu-Yanzu: SSANU Da NASU Sun Janye Yajin Aiki Bayan Ganawa Da Ministan Ilimi

Next Post

Ana Samun Sakamako Mai Kyau A Hadin Gwiwar Dake Tsakanin Sin Da Afirka

Related

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarni Karya Farashin Kayan Abinci A Nijeriya

3 hours ago
Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL
Manyan Labarai

Mele Kyari Ya Bayyana A Ofishin EFCC Kan Zargin Badaƙalar Dala Biliyan 7.2

4 hours ago
Akwai Bukatar Tinubu Ya Rubanya Kokarin Buhari Na Bunkasa Harkokin Noma  -Alhaji Umar
Manyan Labarai

Ranar ‘Yancin Kai: Tinubu Zai Yi Wa ‘Yan Nijeriya Jawabi 1 Ga Oktoba

14 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji 5 Wasu Mutum 10 A Zamfara

16 hours ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

18 hours ago
An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya
Manyan Labarai

An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

20 hours ago
Next Post
Ana Samun Sakamako Mai Kyau A Hadin Gwiwar Dake Tsakanin Sin Da Afirka

Ana Samun Sakamako Mai Kyau A Hadin Gwiwar Dake Tsakanin Sin Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Fashi 3 A Kano, Sun Ƙwato Motar Sata

September 11, 2025
Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

September 11, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Bayar Da Umarni Karya Farashin Kayan Abinci A Nijeriya

September 11, 2025
Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL

Mele Kyari Ya Bayyana A Ofishin EFCC Kan Zargin Badaƙalar Dala Biliyan 7.2

September 11, 2025
Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

September 10, 2025
Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin

Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin

September 10, 2025
Shettima Ya Yaba Wa Uba Sani Kan Kafa Majalisar Ƙwarewa Ta Jihar Kaduna

Shettima Ya Yaba Wa Uba Sani Kan Kafa Majalisar Ƙwarewa Ta Jihar Kaduna

September 10, 2025
Akwai Bukatar Tinubu Ya Rubanya Kokarin Buhari Na Bunkasa Harkokin Noma  -Alhaji Umar

Ranar ‘Yancin Kai: Tinubu Zai Yi Wa ‘Yan Nijeriya Jawabi 1 Ga Oktoba

September 10, 2025
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron CIFTIS Na Shekarar 2025

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron CIFTIS Na Shekarar 2025

September 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.