ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Tattauna Tsakanin Shugaba Xi Na Sin Da Biden Na Amurka

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya tattauna ta wayar tarho da takwaransa na Amurka Joe Biden, inda suka tabo batutuwan da suka shafi dangantakarsu, da ma sauran batutuwan da suke da moriya iri guda.

Tattaunawar ta gudana ne jiya Alhamis bisa rokon shugaban Amurka, Joe Biden.
Yayin tattaunawar, shugaba Xi Jinping ya ce duniya a yanzu na fuskantar matsaloli da sauye-sauye da gibi wajen samun ci gaba da rashin tsaro dake karuwa. Ya kara da cewa, yayin da ake fuskantar sauye-sauye da tashin hankali, kasa da kasa da alummominsu a fadin duniya, na sa ran Sin da Amurka za su ja gaba wajen daukaka zaman lafiya da tsaro da inganta samar da ci gaba da kwanciyar hankali a duniya.

Har ila yau, ya ce bangarorin biyu na bukatar hada hannu wajen rage rikice-rikice a yankunan da taimakawa wajen kawo karshen annobar COVID-19 nan ba da jimawa ba, da rage hadarin hauhawar farashin kayayyaki da rashin aikin yi da tabarbarewar tattalin arziki da kare tsari da dokokin kasa da kasa karkashin jagorancin MDD.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, shugaba Xi ya ce matsayin kasarsa kan batun Taiwan bai sauya ba, kana tabbatar da kare cikakken ’yanci da yankunan kasar Sin, muradi ne mai karfi na alummar Sinawa sama da biliyan 1.4.
A nasa bangaren, shugaba Joe Biden ya ce duniya na kan wata muhimmiyar gaba, kuma hadin gwiwar Sin da Amurka ba alummomin kasashen biyu kadai zai amfanawa ba, har ma da jamaar dukkan kasashen duniya.

Ya ce Amurka na fatan barin kofar tuntubar juna tsakaninta da Sin a bude, domin inganta fahimtar juna da kaucewa rashin fahimta da hada hannu a bangarorin da suke da moriya ta bai daya da kuma tafiyar da bambancin dake tsakaninsu yadda ya kamata.

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Ya kuma nanata cewa, manufar kasar Sin daya tak a duniya ba ta sauya ba a wajen Amurka, kuma ba za ta sauya ba, kana Amurka ba ta goyi bayan ’yancin kan yankin Taiwan. (Mai Fassarawa: Faiza Mustapha)

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara
Daga Birnin Sin

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
'Yansandan Nijeriya

Shirin Sake Fasalin Aikin Rundunar 'Yansandan Nijeriya (Ra'yinmu)

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.