• Leadership Hausa
Saturday, June 3, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Tattauna Tsakanin Shugaba Xi Na Sin Da Biden Na Amurka

by CMG Hausa
10 months ago
in Daga Birnin Sin
0
An Tattauna Tsakanin Shugaba Xi Na Sin Da Biden Na Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya tattauna ta wayar tarho da takwaransa na Amurka Joe Biden, inda suka tabo batutuwan da suka shafi dangantakarsu, da ma sauran batutuwan da suke da moriya iri guda.

Tattaunawar ta gudana ne jiya Alhamis bisa rokon shugaban Amurka, Joe Biden.
Yayin tattaunawar, shugaba Xi Jinping ya ce duniya a yanzu na fuskantar matsaloli da sauye-sauye da gibi wajen samun ci gaba da rashin tsaro dake karuwa. Ya kara da cewa, yayin da ake fuskantar sauye-sauye da tashin hankali, kasa da kasa da alummominsu a fadin duniya, na sa ran Sin da Amurka za su ja gaba wajen daukaka zaman lafiya da tsaro da inganta samar da ci gaba da kwanciyar hankali a duniya.

Har ila yau, ya ce bangarorin biyu na bukatar hada hannu wajen rage rikice-rikice a yankunan da taimakawa wajen kawo karshen annobar COVID-19 nan ba da jimawa ba, da rage hadarin hauhawar farashin kayayyaki da rashin aikin yi da tabarbarewar tattalin arziki da kare tsari da dokokin kasa da kasa karkashin jagorancin MDD.

Bugu da kari, shugaba Xi ya ce matsayin kasarsa kan batun Taiwan bai sauya ba, kana tabbatar da kare cikakken ’yanci da yankunan kasar Sin, muradi ne mai karfi na alummar Sinawa sama da biliyan 1.4.
A nasa bangaren, shugaba Joe Biden ya ce duniya na kan wata muhimmiyar gaba, kuma hadin gwiwar Sin da Amurka ba alummomin kasashen biyu kadai zai amfanawa ba, har ma da jamaar dukkan kasashen duniya.

Ya ce Amurka na fatan barin kofar tuntubar juna tsakaninta da Sin a bude, domin inganta fahimtar juna da kaucewa rashin fahimta da hada hannu a bangarorin da suke da moriya ta bai daya da kuma tafiyar da bambancin dake tsakaninsu yadda ya kamata.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Jaddada Bukatar Gina Kasar Sin Mai Wayewar Kai Ta Zamani

Kasar Sin Ta Bayyana Korafinta Dangane Da Yarjejeniyar Cinikayya Da Aka Kulla Tsakanin Amurka Da Taiwan

Ya kuma nanata cewa, manufar kasar Sin daya tak a duniya ba ta sauya ba a wajen Amurka, kuma ba za ta sauya ba, kana Amurka ba ta goyi bayan ’yancin kan yankin Taiwan. (Mai Fassarawa: Faiza Mustapha)

 

 

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Wasan Kwallon Kwando Ke Haskaka Rayuwar Matashi Hu Yan A Kasar Sin

Next Post

Shirin Sake Fasalin Aikin Rundunar ‘Yansandan Nijeriya (Ra’yinmu)

Related

Xi Jinping Ya Jaddada Bukatar Gina Kasar Sin Mai Wayewar Kai Ta Zamani
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Jaddada Bukatar Gina Kasar Sin Mai Wayewar Kai Ta Zamani

18 hours ago
Kasar Sin Ta Bayyana Korafinta Dangane Da Yarjejeniyar Cinikayya Da Aka Kulla Tsakanin Amurka Da Taiwan
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayyana Korafinta Dangane Da Yarjejeniyar Cinikayya Da Aka Kulla Tsakanin Amurka Da Taiwan

19 hours ago
Taron Tattaunawar Shangri-La Ya Nuna Ra’ayin Tabbatar Da Zaman Lafiya Na Sin
Daga Birnin Sin

Taron Tattaunawar Shangri-La Ya Nuna Ra’ayin Tabbatar Da Zaman Lafiya Na Sin

20 hours ago
An Dakatar Da “Wasan Matsorata” Da Jam’iyyun Siyasan Amurka Suke Yi Amma Damuwa Ta Dore
Daga Birnin Sin

An Dakatar Da “Wasan Matsorata” Da Jam’iyyun Siyasan Amurka Suke Yi Amma Damuwa Ta Dore

22 hours ago
RCEP Ta Fara Aiki A Kasashe 15 Da Suka Sa Hannu Kan Yarjejeniyar
Daga Birnin Sin

RCEP Ta Fara Aiki A Kasashe 15 Da Suka Sa Hannu Kan Yarjejeniyar

23 hours ago
Jami’an Kasuwancin Sin Da Amurka Sun Amince Da Karfafa Muamala
Daga Birnin Sin

Jami’an Kasuwancin Sin Da Amurka Sun Amince Da Karfafa Muamala

24 hours ago
Next Post
'Yansandan Nijeriya

Shirin Sake Fasalin Aikin Rundunar 'Yansandan Nijeriya (Ra'yinmu)

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Bauchi Ya Zama Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP

Gwamnan Bauchi Ya Zama Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP

June 3, 2023
Shanuna Sun Fi Saukin Kiwo A Kan Mulkin Nijeriya – Buhari

Shanuna Sun Fi Saukin Kiwo A Kan Mulkin Nijeriya – Buhari

June 3, 2023
Tinubu Ya Nada Dele Alake A Matsayin Mai Magana Da Yawunsa

Abba Gida-Gida Ya Ba Da Umarnin Rushe Gine-Ginen Da Aka Yi A Filayen Gwamnati

June 3, 2023
Sama Da 280 Ne Suka Mutu, 1000 Suka Jikkata A Hatsarin Jirgin Kasa A Indiya

Sama Da 280 Ne Suka Mutu, 1000 Suka Jikkata A Hatsarin Jirgin Kasa A Indiya

June 3, 2023
Alhazan Abuja Sun Gamu Da Tasku Sakamakon Rashin Samun Masaukai Masu Kyau A Saudiyya 

Za Mu Kwashe Daukacin Maniyyatan Bana 6000 – Hukumar Alhazan Kano

June 3, 2023
Kungiyoyin Da Suka Fi Samun Katin Gargadi A Gasar Firimiya Ta Bana

Kungiyoyin Da Suka Fi Samun Katin Gargadi A Gasar Firimiya Ta Bana

June 3, 2023
Ƴan Sanda A Gombe Sun Kama Matasa 11 Da Ake Zargi Da Kalare

Ƴan Sanda A Gombe Sun Kama Matasa 11 Da Ake Zargi Da Kalare

June 3, 2023
Bello Matawalle Ya Wawashe Kudi Da Motocin Gwamnati — Gwamnatin Zamfara

Bello Matawalle Ya Wawashe Kudi Da Motocin Gwamnati — Gwamnatin Zamfara

June 3, 2023
Ci Gaban Al’umma: Ƙungiyar GMBNI Ta Karrama Ma’aikacin LEADERSHIP Da Wasu

Ci Gaban Al’umma: Ƙungiyar GMBNI Ta Karrama Ma’aikacin LEADERSHIP Da Wasu

June 3, 2023
Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano

Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano

June 3, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.