ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Sake Fasalin Aikin Rundunar ‘Yansandan Nijeriya (Ra’yinmu)

by Sulaiman
4 years ago
'Yansandan Nijeriya

Tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma na daya daga cikin ginshinkin tabbatar da cigaban dukkan al’umma a ko ina a fadin duniyar nan. Haka kuma ‘yansanda ne wadanda aka dora wa nauyin samar da tsaron cikin gida a kowacce kasa a fadin duniya. Rundunar ‘yansandan Nijeriya da Turawan Mulkin Mallaka suka kafa ta gamu da manyan matsaloli tun daga farkon kafata da burin tabbatar da cikakken tsaro ga al’ummar Nijeriya.

Wannan halin da rundunar ta samu kanta ya haifar da sauye-sauye da sake fasali da kokarin kwaskwarima a lokutta daban-daban amma har zuwa yuanzu ba a kai ga samun nasarar da ake bukata ba. Wadannan na daga cikin dalilan da ya sa al’umma suka kasa gamsuwa da yadda ‘yansanda ke gudanar da ayyukansu ba kuma tare da la’akari da dinbin matsalolin da rundunar ke fuskanta ba.

Mambobin Jam’iyyar NNPP 700 Sun Koma Jam’iyyar Labour A Adamawa

ADVERTISEMENT

Ba tare da kokwanto ba, yadda muke ganin tsananin gurbacewar rundunar ‘yansandan mu yana nuna irin yadda al’ummar mu ta gurbace ne. A Nijeriya an kafa rundunar ‘yansanda ne don kare muradun shugabannin mulkin mallaka na Turawa, sun kafa rundunar ne bayan da suka fahimci cewa, in har suka kafa wata runduna ta musamman zai taimaka musu tatsar albarkatun ma’adanai a sassan kasar nan.

A bayyane yake cin hanci da rashawa ya mamaye al’amurra a Nijeriya amma kuma tsananin cin hanci da rashawar da ake samu a rundunar ‘yansandan yana faruwa ne kai tsaye a kan yadda gwamnati da masu ruwa da tsaki suka dauki tafiyar da harkokin rundunar ‘yansandan. Abin dariya ne in har ‘yan Nijeriya za su yi tunanin cewa, ‘yansanda za su zama kamar malaiku da zarar sun sanya kayan sarki na zama ‘yansanda.

LABARAI MASU NASABA

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

A ra’ayinmu, bai kamata ma a zargi ‘yansanda da karbar na goro a kan hanyoyinmu ba daga ‘yan Nijeriya bayan muna sane da cewa, hatta kayan aikin dake jikinsu sune suke saya da kansu tare da dukkan kayan sarkin da suke amfani dasu a fagen gudanar da aikinsu, wadannan kadai sun isa su ingiza su karbar cin hanci da rashawa don kokarin inganta ayyukansu da rayuwarsu, amma anan ba wai muna halasta karbar cin-hancin da suke yi ba ne.
Duk da kokarin da aka yi na sake fasalin rundunar ‘yansandan Nijeriya a lokutta daban-daban, har yanzu rundunar na nan kamar yadda aka santa a shekarun baya, haka na faruwa ne saboda kokarin da aka yi baya kaiwa ga can kasa inda matsalar take. Shirin sake fasalin rundunar da aka yi a baya yana faruwa ne don biyan bukatun masu mulki a lokacin tare da kuma huce takaici da haushin a bin da suke fuskanta.

Shirin sake fasali na baya-bayan nan an yi shi ne a shekarar 1999, amma ba a kai ga cimma manufar aiwatar da sake fasalin ba, wadanda suka hada da bukatar kare rayuwa da dukiyoyin al’ummar Nijeriya ba tare da nuna banbanci ba, sai dai shirin ya gamu da cikas na rashin cikakken kayan aiki da kuma rashin hadin kai daga bangarori daban-daban.

A shekarar 1989, Admiral Murtala Nyako ya jagoranci kwamitin sake fasalin rundunar ‘yansanda amma a duk tsawon wadannan shekarun ba a kai ga cimma wani abin a zo a gani ba na samar da ingantaciyyar rundunar ‘yansanda da al’ummar Nijeriya za su yi alfahari da ita. Bayan shekara biyu kuma, Farfesa Tekena Tamuno ya mika rahonsa na sake fasalin rundunar ‘yansanda amma har yanzu ba a kai ga yin amfani da su ba.

A shekarar 2006 kuma Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo ya kafa wani kwamitin karkashin jagorancin tsohon shugaban rundunar ‘yansadan Nijeriya, Muhammad Danmadami. A shekarar 2008 kuma an kafa sabon kwamiti wanda shima tsohon shugaban rundunar ‘yan sandan Nijeriya, Muhammadu Dikko Yusuf ya jagoranta, ya kuma samu nasarar mika rahoto tattare da shawarwari 125 na yadda za a inganta aikin ‘yansanda amma har zuwa yanzu ba a kai ga aiwatar da daya daga cikin shawarwarin da suka mika ba.

Haka kuma rahoton kwamitin sake fasalin ‘yansanda da shirin ‘Bision 2010’ ya samar bai samu karbuwa ba a hannun mahukunta. Shima kwamitin da Parry Osayande ya jagoranta a shekarar 2012 bai kai labari ba.
Cin zarafin mutane daga ‘yansanda ba abu ba ne da ya kebu ga Nijeriya, abu ne daya game duk duniya. Amma irin yadda ake sanya ido da kuma yadda ake hukunta wadanda aka samu da laifi shi ne yake banbanta, kamar yadda ake samu a kasashe kamar su Kanada Birtaniya wadanda suka yi fice wajen kare hakkin biladam. Irin rashin hukunta ‘yansanda masu cin zarafin al’umma a Nijeriya yake tayar da hankalin al’umma a dukkan lokutta har yake haifar da zanga-zanga kamar yadda muka gani a lokacin ‘EndSARS, wanda hakan kuma yana shafar mutuncin rundunar. A kan haka muke bayar da shawarar samar da rundunar ‘yansanda mai cikakken kayan aiki na zamani tare da biyansu cikakken hakokinsu ta yadda hankalinsu zai fita daga aikata cin hanci da rashawa.

Tabbas lokaci ya yi da za a sake fasalin rundunar ‘yansandan Nijeriya ta yadda za ta yi daidai da tsarin mulkin dimokradiyya, a tabbatar da sun kawo karshen cin zarafin al’umma, musamnman masu karamin karfi.

Yakamata a yi wa tsarin mulki kwaskwarima ta yadda za a iya dauka da korar shugaban rundunar ‘yansanda kai tsaye ba kamar yadda lamarin yake a halin yanzu ba inda sai abin da shugaban kasa ya ga dama, dole ya zamana majalisar kasa ta sanya hannun a kan zabo wanda zai zama shugaban rundunar ‘yansanda su kuma sanya hannu wajen korarsa in ya gaza gudanar da aikinsa.

'Yansandan Nijeriya
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro
Rahotonni

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

September 5, 2026
Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
Rahotonni

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

September 5, 2026
Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
Rahotonni

Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki

September 5, 2026
Next Post
NLC

Yajin Aikin ASUU: Ba Za Mu Sarara Ba Har Sai Gwamnati Ta Magance – NLC

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.