• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Umarci Kwamishinonin ‘Yansanda Su Mika Wa INEC Sakamakon Binciken Laifukan Zabe

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
An Umarci Kwamishinonin ‘Yansanda Su Mika Wa INEC Sakamakon Binciken Laifukan Zabe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sufeton Janar na hukumar ‘yansandan Nijeriya, IGP Usman Baba, ya umarci kwamishinonin ‘yansanda da ke shugabantar Shalkwatar hukumar a jihohi da cewa, dukkanin binciken da suke kan yi na Kesa-kesan da suka shafi karya dokoki da ka’idojin zabe ta shekarar 2022 da aka samu yayin zaben shugaban kasa da ‘yan majalisun tarayya na ranar 25 ga watan Fabrairu su tabbatar sun kammala su. 

 

A cewarsa, bayan sun kuma kammala binciken to su tabbatar sun tura dukkanin fayel-fayel na Kesa-kesan zuwa ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) domin gudanar da su a gaban kuliya mance sabo.

  • ‘Yansanda Sun Ce Cafke Direban Bas Kan Hadarin Jirgin Kasa A Legas

Kazalika, IGP din ya kuma bukaci kwamishinonin da su nemi masu ruwa da tsaki a jihohin domin ganawa da tattauna muhimman batutuwa domin kyautata hidimar tsaro da inganta harkokin zabe.

 

Labarai Masu Nasaba

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

A cewa Baba, hakan zai taimaka wajen jawo kowa da kowa a jika wajen Bada nasa gudunmawar ta fuskacin inganta tsaro domin tabbatar da an samu gudanar da zaben Gwamnoni da ‘yan majalisun jihohi a ranar 18 ga Fabrairu cikin kwanciyar hankali, inganci kuma sahihi.

 

Shugaban na ‘yansandan kasa ya kuma yi kira ga al’ummar kasa da su yi aikin hadin guiwa da hukumar ‘yansandan da sauran hukumomin tsaro domin tabbatar da ingancin tsaro a lokacin zaben.

 

Ya ce akwai bukatar tabbatar da tsaro ga su kansu masu zaben, masu sa Ido, jami’an INEC, kayan aikin zabe, al’umma da dai sauransu, Kuma ya ce za a cimma hakan ne kawai ta hanyar gudunmawar kowa da kowa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsarin Beidou Na Sin Yana Gudanar Da Aikinsa Cikin Aminci

Next Post

Mene Ne Ra’ayin Xi Bayan Kama Aiki A Matsayin Shugaban Sin A Wa’adi Na 3? 

Related

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)
Labarai

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

55 minutes ago
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari
Labarai

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

2 hours ago
Labarai

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

14 hours ago
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)
Labarai

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

15 hours ago
Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu
Labarai

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

17 hours ago
Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama
Labarai

Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

18 hours ago
Next Post
Mene Ne Ra’ayin Xi Bayan Kama Aiki A Matsayin Shugaban Sin A Wa’adi Na 3? 

Mene Ne Ra’ayin Xi Bayan Kama Aiki A Matsayin Shugaban Sin A Wa’adi Na 3? 

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

May 11, 2025
Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

May 10, 2025
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

May 10, 2025
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

May 10, 2025
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

May 10, 2025
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

May 10, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

May 10, 2025
Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.