• English
  • Business News
Thursday, July 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Min Abin Da Zuciya Da Kwakwalwa Ba Za Su Taba Mantawa Ba A Wata Kungiyar Marubuta – Maryam

by Primcess Fatima Zarah Mazadu
1 year ago
in Adabi
0
An Yi Min Abin Da Zuciya Da Kwakwalwa Ba Za Su Taba Mantawa Ba A Wata Kungiyar Marubuta – Maryam
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

A kashi na biyu na tattaunawa da MARYAM ABDUL’AZIZ wacce aka fi sani da MAI KOSAI ta bayyana wasu nasarori da kalubalen da suka ci mata tuwo a kwarya a kan harkar rubuta kamar yadda za ku ji daga hirarsu da PRINCESS FATIMA ZARAH MAZADU kamar haka:

Kin rubuta labari sun kai guda nawa?

To gaskiya labaraina suna da yawa, don a kwai wadanda a littafi ne na rubuta su, sun kai guda biyar, sai kuma lokacin dana fara rike babbar waya na fara rubutu a online, to suma na online din a kwai cikakku da wadanda ba cikakku ba, ma’ana a kwai wadanda na fara ban kai ga kammala rubutawa ba, idan zan hade su duka har wadancan na bayan to sun kai 15 a haka ma ban da gajerun labarai dana rubuta.

A cikin labarun da ki ka rubuta, wanne ki ka fi so?

Gaskiya na fi kaunar ‘Biyayya’ saboda na gina littafin ne kan yadda jaruman suka jajirce wajen yi wa iyayensu biyayya a kan abin da ba rayukansu ke so ba, wanda daga karshe suka ga ribar hakan, kuma suka ga ribar hakuri da juriyar abin da suka yi.

Wane labari ne ya fi baki wahala wajen rubutawa?

Labarin ‘Hafsatul-Kiram’ Saboda na sha bincike sosai a kansa, kuma har yanzu ban ma kammala shi ba, don bana jin ko damba na daura a kansa.

Cikin labarun da kika rubuta ko a kwai wanda ki ka buga ciki?

Eh! a kwai wanda na buga, kuma ina saka ran sake buga wasu in sha Allah.

Wane irin nasarori ki ka samu hame da rubutu?

Alhamdu lillah! Na samu nasarori da dama a harkar rubutu, ba abin da zan ce da Allah Madaukakin Sarki sai godiya, domin wannan wata babbar ni’ima ce ya ba ni da ba kowa ya ke bawa ba.

Ko a kwai wani kalubale da kika fuskanta game da rubutu?

Eh! Na fuskanci kalubale musamman a lokacin dana fara rubutun online, duk da dai wacce ta yi min jagora ba ta cuce ni ba, ba ta kuma rage ni da komai ba, don tsakanina da ita har yau har gobe sai godiya da fatan alkhairi. Sai dai shiga ta wata kungiya ya sa na ji na karaya har ina jin kawai gara na hakura na ajjiye harkar rubutu kwata-kwata, saboda an yi min abu ma fi soyuwar ciwon da zuciya da kwakwalwa ba za su kasa mancewa ba. Bangaren masu karatu tsakanina da su sai godiya, don wasu ma baka san su ba haka za su kiraka ko su yi maka magana su ce suna son littafinka. Duk da na taba fuskantar wani kalubale ta bangarensu wanda abun ya ba ni mamaki sosai. Na yi wani littafin kudi ne, sai wata ta biyo ni ‘pribate’ tana tambayata, “Wai ke me ya sa ba kya saka ‘romantic’ a littafinki, da sai ya fi ba da citta? Ina son siyan wannan amma na ga alama kamar babu rakashewa a ciki.”

Abun ya ba ni dariya ya ba ni mamaki, wato idan babu batsa ba za ta siya ba ke nan? To ire-irensu ina samu da dama, da kuma makamanta haka.

Wane abu ne ya taba faruwa da ke na farin ciki ko akasin hakan wanda ba za ki manta da shi ba game da rubutu?

Ba a rasa ba, amma ni idan ma an so a bata min rai kaucewa nake yi, saboda idan ka ce al’amarin mutane za ka yi ta sakawa a gaba to zuciyarka ce za ta haye ta suntuma ta fashe kamar wata bom. Ana yabawa sosai, kuma iyayena sune na farkon da suke yabawa bana damuwa da sauran jama’a idan ba su yaba ba, amma duk da haka ana yabawa daidai gwargwado.

Me ya fi saka ki farin ciki game da rubutu?

Idan ina rubutu na kan tuna baya, lokacin da nake rubutu a boye kamar wacce ta yi abin rashin arziki take tsoron a kamata, to idan ina rubutu na kan tuna sai na ji na dara na shiga kogin walwala.

Ya ki ka dauki rubutu a wajenki?

Gaskiya rubutu a wajena wani babban al’amari ne, wanda ina ganinsa da matukar muhimmanci sosai fiye da kima.

Bayan rubutu kina yin sana’a?

Eh! ina taba harkokin kasuwanci.

Ya kike iya hada rubutu da kuma kasuwanci?

To ina ware lokutan rubutu duk da wani lokacin kwatsam zan ji ‘idea’ ta fado min, daman a kwai biro da takarda kusa da ni, zan maza na rubuta, ko na shigar a wayata. Amma dai duk ina iya hada su waje guda tunda kasuwanci ne kake na online ba shago za ka fita ko kasuwa ba.

Kamar da wane lokacin kika fi jin dadin yin rubutu?

Na fi jin dadin yin rubutu da daddare, kowa ya yi bacci koda Asuba.

Me za ki ce da makaranta littafinki?

Babu abin da zan ce da su sai fatan alkhairi.

Ko kina da wadanda za ki gaisar?

Na farko iyayena, da kannena, na biyu maigidana, na uku Malamaina, na hudu Marubuta gabadayansu kaf! ban ware ko guda ba, na biyar ‘Yan’uwa da abokan arziki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdabiMarubutaZuciya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sanata Iya Abbas Ya Jajantawa Mutanen Da Iftila’in Iskar Hadarin Ruwa Ta Shafa A Hong

Next Post

Rawar Da Iyaye Ke Takawa Wajen Taimaka Wa ‘Ya’ya Cimma Burinsu Na Karatu (1)

Related

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
Adabi

Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili

3 months ago
Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa
Al'adu

Dr. Maryam Yola Ta Zama Farfesa Mace Ta Farko Kan Magungunan Gargajiya Da Al’adun Hausa

7 months ago
Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya
Adabi

Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya

8 months ago
Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk
Adabi

Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk

9 months ago
Mahaifiyata Ce Ta Karfafe Ni Shiga Harkar Rubutu –Maryam Faruk
Adabi

Mahaifiyata Ce Ta Karfafe Ni Shiga Harkar Rubutu –Maryam Faruk

9 months ago
Yadda Malaminmu Na Hausa Ya Karfafa Min Kwarin Gwiwar Fara Rubutu – Salma Ahmad
Adabi

Yadda Malaminmu Na Hausa Ya Karfafa Min Kwarin Gwiwar Fara Rubutu – Salma Ahmad

11 months ago
Next Post
Rawar Da Iyaye Ke Takawa Wajen Taimaka Wa ‘Ya’ya Cimma Burinsu Na Karatu (1)

Rawar Da Iyaye Ke Takawa Wajen Taimaka Wa ‘Ya’ya Cimma Burinsu Na Karatu (1)

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

July 30, 2025
Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

July 30, 2025
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

July 30, 2025
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

July 30, 2025
Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

July 30, 2025
Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

July 30, 2025
Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

July 30, 2025
Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

July 30, 2025
Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

July 30, 2025
Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

July 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.