• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Wa Sama Da Mutum 130 Gwajin Cutar Hanta Kyauta A Kano

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Rahotonni
0
An Yi Wa Sama Da Mutum 130 Gwajin Cutar Hanta Kyauta A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cibiyar lafiya ta MGK Healthcare ta gudanar da taron wayar da kan al’umma tare da yi musu gwajin cutar hanta kyauta a jihar Kano inda mutu sama da 130 suka amfana.

Babban Jami’in gudanarwa na MGK Healthcare, Pharm. Isma’il Usman wanda ya wakilci babban shugaban asibitin, Muhammad Garba, ya shaidawa manema labarai jimkadan bayan kammala aikin da ya gudana a karshen mako a harabar asibitin a Kano, ya ce sun shirya wannan taron ne domin wayar da kan al’umma kan cutar ta hanta tare da karfafa su akan muhimmancin yin gwajin cutar domin samun kariya daga kamuwa da cutar tare da sanin maganin cutar tare da kuma yi musu gwajin cutar a kyauta.

  • Yau Alhamis Za A Yanke Hukunci Kan Malamin Da Ake Zargi Da Yi Wa Dalibarsa Kisan Gilla A Kano

Ya ce: “Domin mu tuna ranar Hanta ta duniya. Ranar hanta ta duniya ana tunawa da shi ne a ranar 28 ga watan Yulin kowacce shekara. Sannan a kowacce shekara akwai take da hukumar lafiya ta duniya take fitarwa na abin da za a maida hankali a kan shi. A wannan shekarar hukumar lafiya ta duniya ta fitar da sabon take na ‘kusanto da karfafa gwaji da kuma samar da magani ga mutane’”, ya lurantar.

Ya ci gaba da cewa; “Mun kalli wannan wani abu ne da za mu bayar da gudummawa wajen samar da lafiyar al’umma domin ganin cewar an kiyaye mutane daga kamuwa daga wannan cutar. Wanda suke da ita kuma a yi kokarin gano ta a kuma samar musu da hanyar da za su iya samun magani da shawarwari”.

Cutar Hanta

Labarai Masu Nasaba

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Da ya juyo dangane da shawarwarin da suke bai wa al’umma kan wannan cutar kuwa, Pharm Isma’il ya ce; “Cutar hanta cuta ce wacce mutane da dama su na dauke da ita ba tare da sun sani ba. Wasu da dama su na yawo da ita ba su san ma suna dauke da ita ba. Kididdiga ta nuna cewar akalla duk dakika 30 ana samun mutum daya da yake mutuwa a dalilin cutar da ke da alaka da cutar hanta”, ya nusasshe.

“Shawararmu ga al’umma shi ne su farga su kuma yi kokarin zuwa asibitoci domin a tantance su a tabbatar musu ko suna da wannan cuta ko ba su da shi.”

Ya yi takaitaccen bayani dangane da rabe-raben cutar hanta da yadda ake kamuwa da ita. Tare da zayyano irin aikin da hanta take yi a jikin dan Adam. “Hanta ita ke sarrafa abincin da muke ci da sha na yau da kullum, ta maida su yadda za su yi aiki sannan ta gabatar da su ga jiki. Wadansu abubuwan da za su iya illata jikin mutum ita ke canza su ta maida su yadda ba zai illata jikin ba,” ya lurantar.

Cutar Hanta

Ya nuna illar dake cikin a ce hantar mutum ta kamu da ciwo, inda ya ce; “daga lokacin da hanta ta illatu, zai zama dukkanin bangarorin jikin mutum zai zamo cikin illa.”

A karshe ya yi bayani dangane da ayyukan asibitin na MGK Healthcare, inda ya ce asibiti ne na kwararru da yake yin ayyuka daban-daban. Kuma suna da kananu da manyan likitoci da suke duba marasa lafiya daban-daban wadanda suka hada da masu zuwa a duba su su koma gida, da ma wadanda ake kwantar da su har sai sun samu lafiya.

Sannan ya ce daga cikin ayyukansu suna da bangaren masu kula da ciwon hakori, bangaren bayar da magunguna, bangaren gwaje-gwajen cututtuka manya da kanana, bangaren da ke haska cututtukan dake jikin mutum, sannan suna yin tiyatar da ya hada da na kashi, karbar haihuwa, na cututtuka, na kwakwalwa da jijiya da kuma na zuciya da sauran su.

“Sannan muna dauko marasa lafiyar da suke da bukatar taimakon gaggawa zuwa asibiti da motar daukar marasa lafiya wanda ake tafiya da ma’aikatan asibitin a cikinta. Sannan muna da gidauniyyar da take bai wa al’umma marasa karfi gudummawa a bangaren ilimi, kiwon lafiya da kuma muhalli”.

Har wala yau ya ce suna da lasisi a bangaren inshorar lafiya da gwamnatin Tarayya da ta jihar Kano da ma kamfanoni, wadanda ma’aikatan dake karkashin wadannan ke zuwa asibitin ana kula da lafiyarsu musamman wadanda suke karkashin inshorar lafiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Amurka Ta Kashe Shugaban Al-Qaeda A Wani Hari Da Ta Kai Afghanistan

Next Post

Malaman KASU Sun Janye Yajin Aiki Bayan Barazanar El-Rufa’i 

Related

Cutar Hanta
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

11 hours ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

2 days ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 week ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 week ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Next Post
Malaman KASU Sun Janye Yajin Aiki Bayan Barazanar El-Rufa’i 

Malaman KASU Sun Janye Yajin Aiki Bayan Barazanar El-Rufa’i 

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.