• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Wa Sama Da Mutum 130 Gwajin Cutar Hanta Kyauta A Kano

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Rahotonni
0
An Yi Wa Sama Da Mutum 130 Gwajin Cutar Hanta Kyauta A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cibiyar lafiya ta MGK Healthcare ta gudanar da taron wayar da kan al’umma tare da yi musu gwajin cutar hanta kyauta a jihar Kano inda mutu sama da 130 suka amfana.

Babban Jami’in gudanarwa na MGK Healthcare, Pharm. Isma’il Usman wanda ya wakilci babban shugaban asibitin, Muhammad Garba, ya shaidawa manema labarai jimkadan bayan kammala aikin da ya gudana a karshen mako a harabar asibitin a Kano, ya ce sun shirya wannan taron ne domin wayar da kan al’umma kan cutar ta hanta tare da karfafa su akan muhimmancin yin gwajin cutar domin samun kariya daga kamuwa da cutar tare da sanin maganin cutar tare da kuma yi musu gwajin cutar a kyauta.

  • Yau Alhamis Za A Yanke Hukunci Kan Malamin Da Ake Zargi Da Yi Wa Dalibarsa Kisan Gilla A Kano

Ya ce: “Domin mu tuna ranar Hanta ta duniya. Ranar hanta ta duniya ana tunawa da shi ne a ranar 28 ga watan Yulin kowacce shekara. Sannan a kowacce shekara akwai take da hukumar lafiya ta duniya take fitarwa na abin da za a maida hankali a kan shi. A wannan shekarar hukumar lafiya ta duniya ta fitar da sabon take na ‘kusanto da karfafa gwaji da kuma samar da magani ga mutane’”, ya lurantar.

Ya ci gaba da cewa; “Mun kalli wannan wani abu ne da za mu bayar da gudummawa wajen samar da lafiyar al’umma domin ganin cewar an kiyaye mutane daga kamuwa daga wannan cutar. Wanda suke da ita kuma a yi kokarin gano ta a kuma samar musu da hanyar da za su iya samun magani da shawarwari”.

Cutar Hanta

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

Da ya juyo dangane da shawarwarin da suke bai wa al’umma kan wannan cutar kuwa, Pharm Isma’il ya ce; “Cutar hanta cuta ce wacce mutane da dama su na dauke da ita ba tare da sun sani ba. Wasu da dama su na yawo da ita ba su san ma suna dauke da ita ba. Kididdiga ta nuna cewar akalla duk dakika 30 ana samun mutum daya da yake mutuwa a dalilin cutar da ke da alaka da cutar hanta”, ya nusasshe.

“Shawararmu ga al’umma shi ne su farga su kuma yi kokarin zuwa asibitoci domin a tantance su a tabbatar musu ko suna da wannan cuta ko ba su da shi.”

Ya yi takaitaccen bayani dangane da rabe-raben cutar hanta da yadda ake kamuwa da ita. Tare da zayyano irin aikin da hanta take yi a jikin dan Adam. “Hanta ita ke sarrafa abincin da muke ci da sha na yau da kullum, ta maida su yadda za su yi aiki sannan ta gabatar da su ga jiki. Wadansu abubuwan da za su iya illata jikin mutum ita ke canza su ta maida su yadda ba zai illata jikin ba,” ya lurantar.

Cutar Hanta

Ya nuna illar dake cikin a ce hantar mutum ta kamu da ciwo, inda ya ce; “daga lokacin da hanta ta illatu, zai zama dukkanin bangarorin jikin mutum zai zamo cikin illa.”

A karshe ya yi bayani dangane da ayyukan asibitin na MGK Healthcare, inda ya ce asibiti ne na kwararru da yake yin ayyuka daban-daban. Kuma suna da kananu da manyan likitoci da suke duba marasa lafiya daban-daban wadanda suka hada da masu zuwa a duba su su koma gida, da ma wadanda ake kwantar da su har sai sun samu lafiya.

Sannan ya ce daga cikin ayyukansu suna da bangaren masu kula da ciwon hakori, bangaren bayar da magunguna, bangaren gwaje-gwajen cututtuka manya da kanana, bangaren da ke haska cututtukan dake jikin mutum, sannan suna yin tiyatar da ya hada da na kashi, karbar haihuwa, na cututtuka, na kwakwalwa da jijiya da kuma na zuciya da sauran su.

“Sannan muna dauko marasa lafiyar da suke da bukatar taimakon gaggawa zuwa asibiti da motar daukar marasa lafiya wanda ake tafiya da ma’aikatan asibitin a cikinta. Sannan muna da gidauniyyar da take bai wa al’umma marasa karfi gudummawa a bangaren ilimi, kiwon lafiya da kuma muhalli”.

Har wala yau ya ce suna da lasisi a bangaren inshorar lafiya da gwamnatin Tarayya da ta jihar Kano da ma kamfanoni, wadanda ma’aikatan dake karkashin wadannan ke zuwa asibitin ana kula da lafiyarsu musamman wadanda suke karkashin inshorar lafiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Amurka Ta Kashe Shugaban Al-Qaeda A Wani Hari Da Ta Kai Afghanistan

Next Post

Malaman KASU Sun Janye Yajin Aiki Bayan Barazanar El-Rufa’i 

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

3 weeks ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

4 weeks ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

4 weeks ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

4 weeks ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

4 weeks ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
Malaman KASU Sun Janye Yajin Aiki Bayan Barazanar El-Rufa’i 

Malaman KASU Sun Janye Yajin Aiki Bayan Barazanar El-Rufa’i 

LABARAI MASU NASABA

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.