• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Wa Sama Da Mutum 130 Gwajin Cutar Hanta Kyauta A Kano

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Rahotonni
0
An Yi Wa Sama Da Mutum 130 Gwajin Cutar Hanta Kyauta A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cibiyar lafiya ta MGK Healthcare ta gudanar da taron wayar da kan al’umma tare da yi musu gwajin cutar hanta kyauta a jihar Kano inda mutu sama da 130 suka amfana.

Babban Jami’in gudanarwa na MGK Healthcare, Pharm. Isma’il Usman wanda ya wakilci babban shugaban asibitin, Muhammad Garba, ya shaidawa manema labarai jimkadan bayan kammala aikin da ya gudana a karshen mako a harabar asibitin a Kano, ya ce sun shirya wannan taron ne domin wayar da kan al’umma kan cutar ta hanta tare da karfafa su akan muhimmancin yin gwajin cutar domin samun kariya daga kamuwa da cutar tare da sanin maganin cutar tare da kuma yi musu gwajin cutar a kyauta.

  • Yau Alhamis Za A Yanke Hukunci Kan Malamin Da Ake Zargi Da Yi Wa Dalibarsa Kisan Gilla A Kano

Ya ce: “Domin mu tuna ranar Hanta ta duniya. Ranar hanta ta duniya ana tunawa da shi ne a ranar 28 ga watan Yulin kowacce shekara. Sannan a kowacce shekara akwai take da hukumar lafiya ta duniya take fitarwa na abin da za a maida hankali a kan shi. A wannan shekarar hukumar lafiya ta duniya ta fitar da sabon take na ‘kusanto da karfafa gwaji da kuma samar da magani ga mutane’”, ya lurantar.

Ya ci gaba da cewa; “Mun kalli wannan wani abu ne da za mu bayar da gudummawa wajen samar da lafiyar al’umma domin ganin cewar an kiyaye mutane daga kamuwa daga wannan cutar. Wanda suke da ita kuma a yi kokarin gano ta a kuma samar musu da hanyar da za su iya samun magani da shawarwari”.

Cutar Hanta

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

Da ya juyo dangane da shawarwarin da suke bai wa al’umma kan wannan cutar kuwa, Pharm Isma’il ya ce; “Cutar hanta cuta ce wacce mutane da dama su na dauke da ita ba tare da sun sani ba. Wasu da dama su na yawo da ita ba su san ma suna dauke da ita ba. Kididdiga ta nuna cewar akalla duk dakika 30 ana samun mutum daya da yake mutuwa a dalilin cutar da ke da alaka da cutar hanta”, ya nusasshe.

“Shawararmu ga al’umma shi ne su farga su kuma yi kokarin zuwa asibitoci domin a tantance su a tabbatar musu ko suna da wannan cuta ko ba su da shi.”

Ya yi takaitaccen bayani dangane da rabe-raben cutar hanta da yadda ake kamuwa da ita. Tare da zayyano irin aikin da hanta take yi a jikin dan Adam. “Hanta ita ke sarrafa abincin da muke ci da sha na yau da kullum, ta maida su yadda za su yi aiki sannan ta gabatar da su ga jiki. Wadansu abubuwan da za su iya illata jikin mutum ita ke canza su ta maida su yadda ba zai illata jikin ba,” ya lurantar.

Cutar Hanta

Ya nuna illar dake cikin a ce hantar mutum ta kamu da ciwo, inda ya ce; “daga lokacin da hanta ta illatu, zai zama dukkanin bangarorin jikin mutum zai zamo cikin illa.”

A karshe ya yi bayani dangane da ayyukan asibitin na MGK Healthcare, inda ya ce asibiti ne na kwararru da yake yin ayyuka daban-daban. Kuma suna da kananu da manyan likitoci da suke duba marasa lafiya daban-daban wadanda suka hada da masu zuwa a duba su su koma gida, da ma wadanda ake kwantar da su har sai sun samu lafiya.

Sannan ya ce daga cikin ayyukansu suna da bangaren masu kula da ciwon hakori, bangaren bayar da magunguna, bangaren gwaje-gwajen cututtuka manya da kanana, bangaren da ke haska cututtukan dake jikin mutum, sannan suna yin tiyatar da ya hada da na kashi, karbar haihuwa, na cututtuka, na kwakwalwa da jijiya da kuma na zuciya da sauran su.

“Sannan muna dauko marasa lafiyar da suke da bukatar taimakon gaggawa zuwa asibiti da motar daukar marasa lafiya wanda ake tafiya da ma’aikatan asibitin a cikinta. Sannan muna da gidauniyyar da take bai wa al’umma marasa karfi gudummawa a bangaren ilimi, kiwon lafiya da kuma muhalli”.

Har wala yau ya ce suna da lasisi a bangaren inshorar lafiya da gwamnatin Tarayya da ta jihar Kano da ma kamfanoni, wadanda ma’aikatan dake karkashin wadannan ke zuwa asibitin ana kula da lafiyarsu musamman wadanda suke karkashin inshorar lafiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Amurka Ta Kashe Shugaban Al-Qaeda A Wani Hari Da Ta Kai Afghanistan

Next Post

Malaman KASU Sun Janye Yajin Aiki Bayan Barazanar El-Rufa’i 

Related

Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

3 days ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

7 days ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

1 week ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

1 week ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

2 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

2 weeks ago
Next Post
Malaman KASU Sun Janye Yajin Aiki Bayan Barazanar El-Rufa’i 

Malaman KASU Sun Janye Yajin Aiki Bayan Barazanar El-Rufa’i 

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

September 14, 2025
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.