• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Zargi Masari Zai Kashe Miliyan 500 Don Tarbar Buhari A Katsina

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
in Manyan Labarai
0
An Zargi Masari Zai Kashe Miliyan 500 Don Tarbar Buhari A Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar adawa ta PDP a Jihar Katsina, ta zargi Gwamnan Jihar, Aminu Bello Masari, da bayar da umarnin kashe sama da Naira miliyan 500 daga asusun kananan hukumomin jihar don tarbar shugaban kasa Muhammadu Buhari zuwa jihar.

Ana sa ran Buhari zai kai ziyarar aiki ta kwanaki biyu, daga ranar 26 zuwa 27 ga watan Janairu a jihar.

  • Limaman Masallatan Juma’a Na Arewa Sun Ayyana Goyon Bayansu Ga Takarar Tinubu Da Shettima 
  • Allah Ya Yi Wa Jarumin Kannywood, Abdulwahab Awarwasa Rasuwa

Sai dai jam’iyyar adawa ta PDP a jihar ta soki wannan shiri, inda ta alakanta da shi a matsayin almubazzaranci.

Shugaban kungiyar yada manufofin Atiku da Lado, Alhaji Lawal Ɗan Ade ya yi zargin cewa za a kashe kudaden ba bisa ka’ida ba.

Alhaji Lawal Dan Ade, ne ya shaida wa manema labarai cikin wata takarda da ya ce gwamnan jihar, ya amince tare da sahale kashe kudaden.

Labarai Masu Nasaba

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

 

Masari
Alhaji Lawal Dan Ade

A cewarsa takardar wadda aka turawa Kwamishinan kananan hukumomi da masarautu na jihar, ta nuna cewa za a cire miliyan N14,695,588.00 daga kowace karamar hukuma.

Adadin kudin da za a cire daga jihohin baki daya zai kai kimanin Naira miliyan N499,650,000.00

“Idan har wannan zargi da muke yi, ya tabbata muna kira da babbar murya cewa Katsinawa su fito su nuna rashin amincewarsu kan wannan badakala da aka shirya domin zuwan shugaba Buhari Jihar Katsina” in shi

Ya kuma kara da cewa ya kamata shugaba Buhari, ya nesanta kansa da wannan badakala da ake shirin aikatawa a jihar.

A cewarsa wadannan kudede akwai abubuwa da yawa da za a iya da su musamman wajen magance matsalolin da suka shafi makarantu da asibitoci da ‘yan gudun hijira da sauransu.

Sai dai Kwamishinan kananan hukumomi da masarautu na Jihar Katsina, Ya’u Umar Gwajo-gwajo, ya musanta wannan zargi, inda ya ce har yanzu idonsa bai ga wannan takarda da ake magana ba.

Kwamishinan ya sha alwashin bin diddigin wannan takarda da ake zargin an cire wadannan kudade.

Masari
Ya’u Umar Gwajo-gwajo

Ya ce zai bayyana abin da ake ciki game da maganar kudaden.

“Kamar yadda na fada cikin satin da ya gabata cewa kudaden kananan hukumomi suna nan ba gara ba zago, to har yanzu sunan nan, babu wata magana kan cewar za a cire wasu kudede domin zuwan shugaban kasa Jihar Katsina,” in ji shi.

Ana sa ran shugaba Buhari zai kai ziyarar ne don bude wasu manyan ayyuka da gwamnatin jihar ta yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariKatsinaKudin Kananan HukumomiMasariTarbaZargiZiyarar Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Limaman Masallatan Juma’a Na Arewa Sun Ayyana Goyon Bayansu Ga Takarar Tinubu Da Shettima 

Next Post

Kasuwar Tafiye-Tafiyen Sin Ta Samu Farfadowa A Yayin Bikin Bazara 

Related

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

12 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

13 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

15 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

16 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

17 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

22 hours ago
Next Post
Kasuwar Tafiye-Tafiyen Sin Ta Samu Farfadowa A Yayin Bikin Bazara 

Kasuwar Tafiye-Tafiyen Sin Ta Samu Farfadowa A Yayin Bikin Bazara 

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.