• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Fargaba An Sha Kwana Da Shinkafar Gwamnatin Tarayya A Bauchi, Gombe, Da Dutse

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Shinkafa

Mazauna Bauchi, Gombe, da Dutse sun bayyana damuwarsu kan zargin karkatar da tallafin shinkafar Gwamnatin Tarayya da ake nufi don rage wa mutane raɗaɗin tsadar rayuwa.

Gwamnatin ta ware tireloli 20 na shinkafa ga jihohi 36 tare da sauran kayan agaji a matsayin tallafi ga marasa galihu saboda ƙalubalen tattalin arziƙin da ake fuskanta. Amma mutane a waɗannan jihohi suna zargin cewa an karkatar da rarraba kayan zuwa wani wajen daban.

  • Shin Barcelona Da Atletico Madrid Zu Su Iya Dakatar Da Real Madrid A La Liga?
  • Shugaba Tinubu Ya Yi Alhinin Rasuwar Sarkin Ningi

A Dutse, Jihar Jigawa, suna zargin jami’an gwamnati da fifita magoya bayan jam’iyyarsu wajen rabon tallafin. Alhaji Muhammadu Hamza ya soki yadda aka gudanar da rabon, inda ya ce iyalai da dama masu buƙata basu samu komai ba.

Haka zalika, Malam Musa Ali da Hajiya Maimuna sun zargi jami’ai da damfarar talakawa daga samun tallafin da ya dace da su.

A Bauchi, jinkirin rarraba shinkafar ya tada hankalin mazauna da ke jin tsoron ko an boye tallafin. Malam Sani Muazu ya ce jinkirin ya kara tsananta matsalar abinci ga talakawa. Shugaban ƙungiyar hada kan ƙungiyoyin Jama’a na Bauchi (BASNEC), Garba Jinjiri, ya bayyana irin wannan damuwa tare da bayyana rashin jin daɗin cire ƙungiyoyin jama’a daga kwamitin rabon kayan.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar NUJ Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

Wani babban jami’in Ma’aikatar Harkokin jin Kai ta Jihar Bauchi, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce har yanzu jihar ba ta samu tallafin ba, amma ya tabbatar da cewa idan an samu za a rarraba kai tsaye.

A Gombe, mazauna irinsu Mrs. Audu Alheri da Musa Ahmed sun yi ikirarin cewa ba a raba tallafin shinkafar gwamnatin tarayya ba, inda wasu ke zaton an boye kayan.

Shugaban Gombe Network of Civil Society (GONET), Yusuf Ibrahim, ya yaba da kokarin gwamnatin jihar, amma ya nemi inganta gaskiya a tsarin.

Yayin da wannan ce-ce-ku-ce ke ci gaba da faruwa, mutane suna kira ga gwamnatocin jihohin da su tabbatar tallafin ya kai ga waɗanda suka fi buƙata, tare da gudanar da tsarin rarraba tallafin cikin gaskiya da adalci.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisar NUJ Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa
Labarai

Majalisar NUJ Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 22, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025
Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina
Labarai

Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

October 22, 2025
Next Post
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

NYSC Ta Mayar Da Sansaninta Na Bauchi Zuwa Kwalejin Kangere 

LABARAI MASU NASABA

Majalisar NUJ Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

Majalisar NUJ Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 22, 2025
Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

October 22, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025
Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

October 22, 2025
An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

October 22, 2025
Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

October 22, 2025
Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

October 22, 2025
Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

October 22, 2025
Tanka

Majalisa Ta Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kai Agajin Gaggawa Ga Waɗanda Fashewar Tanka Ta Shafa A Neja

October 22, 2025
Zimbabwe Ta Jinjinawa Jarin Sin A Matsayin Wanda Ya Bunkasa Masana’atun Samar Da Siminti A Kasar

Zimbabwe Ta Jinjinawa Jarin Sin A Matsayin Wanda Ya Bunkasa Masana’atun Samar Da Siminti A Kasar

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.