ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Fargaba An Sha Kwana Da Shinkafar Gwamnatin Tarayya A Bauchi, Gombe, Da Dutse

by Abubakar Sulaiman
2 years ago
Shinkafa

Mazauna Bauchi, Gombe, da Dutse sun bayyana damuwarsu kan zargin karkatar da tallafin shinkafar Gwamnatin Tarayya da ake nufi don rage wa mutane raɗaɗin tsadar rayuwa.

Gwamnatin ta ware tireloli 20 na shinkafa ga jihohi 36 tare da sauran kayan agaji a matsayin tallafi ga marasa galihu saboda ƙalubalen tattalin arziƙin da ake fuskanta. Amma mutane a waɗannan jihohi suna zargin cewa an karkatar da rarraba kayan zuwa wani wajen daban.

  • Shin Barcelona Da Atletico Madrid Zu Su Iya Dakatar Da Real Madrid A La Liga?
  • Shugaba Tinubu Ya Yi Alhinin Rasuwar Sarkin Ningi

A Dutse, Jihar Jigawa, suna zargin jami’an gwamnati da fifita magoya bayan jam’iyyarsu wajen rabon tallafin. Alhaji Muhammadu Hamza ya soki yadda aka gudanar da rabon, inda ya ce iyalai da dama masu buƙata basu samu komai ba.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, Malam Musa Ali da Hajiya Maimuna sun zargi jami’ai da damfarar talakawa daga samun tallafin da ya dace da su.

A Bauchi, jinkirin rarraba shinkafar ya tada hankalin mazauna da ke jin tsoron ko an boye tallafin. Malam Sani Muazu ya ce jinkirin ya kara tsananta matsalar abinci ga talakawa. Shugaban ƙungiyar hada kan ƙungiyoyin Jama’a na Bauchi (BASNEC), Garba Jinjiri, ya bayyana irin wannan damuwa tare da bayyana rashin jin daɗin cire ƙungiyoyin jama’a daga kwamitin rabon kayan.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Wani babban jami’in Ma’aikatar Harkokin jin Kai ta Jihar Bauchi, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce har yanzu jihar ba ta samu tallafin ba, amma ya tabbatar da cewa idan an samu za a rarraba kai tsaye.

A Gombe, mazauna irinsu Mrs. Audu Alheri da Musa Ahmed sun yi ikirarin cewa ba a raba tallafin shinkafar gwamnatin tarayya ba, inda wasu ke zaton an boye kayan.

Shugaban Gombe Network of Civil Society (GONET), Yusuf Ibrahim, ya yaba da kokarin gwamnatin jihar, amma ya nemi inganta gaskiya a tsarin.

Yayin da wannan ce-ce-ku-ce ke ci gaba da faruwa, mutane suna kira ga gwamnatocin jihohin da su tabbatar tallafin ya kai ga waɗanda suka fi buƙata, tare da gudanar da tsarin rarraba tallafin cikin gaskiya da adalci.

Shinkafa
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci, Sun Kashe Wani Yaro A Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Babachir Lawal Ya Fice Daga ADC, Ya Zargi Atiku Da Murɗe Zaben Fidda Gwani

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

NYSC Ta Mayar Da Sansaninta Na Bauchi Zuwa Kwalejin Kangere 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.