ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Fargaba An Sha Kwana Da Shinkafar Gwamnatin Tarayya A Bauchi, Gombe, Da Dutse

by Abubakar Sulaiman
2 years ago
Shinkafa

Mazauna Bauchi, Gombe, da Dutse sun bayyana damuwarsu kan zargin karkatar da tallafin shinkafar Gwamnatin Tarayya da ake nufi don rage wa mutane raɗaɗin tsadar rayuwa.

Gwamnatin ta ware tireloli 20 na shinkafa ga jihohi 36 tare da sauran kayan agaji a matsayin tallafi ga marasa galihu saboda ƙalubalen tattalin arziƙin da ake fuskanta. Amma mutane a waɗannan jihohi suna zargin cewa an karkatar da rarraba kayan zuwa wani wajen daban.

  • Shin Barcelona Da Atletico Madrid Zu Su Iya Dakatar Da Real Madrid A La Liga?
  • Shugaba Tinubu Ya Yi Alhinin Rasuwar Sarkin Ningi

A Dutse, Jihar Jigawa, suna zargin jami’an gwamnati da fifita magoya bayan jam’iyyarsu wajen rabon tallafin. Alhaji Muhammadu Hamza ya soki yadda aka gudanar da rabon, inda ya ce iyalai da dama masu buƙata basu samu komai ba.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, Malam Musa Ali da Hajiya Maimuna sun zargi jami’ai da damfarar talakawa daga samun tallafin da ya dace da su.

A Bauchi, jinkirin rarraba shinkafar ya tada hankalin mazauna da ke jin tsoron ko an boye tallafin. Malam Sani Muazu ya ce jinkirin ya kara tsananta matsalar abinci ga talakawa. Shugaban ƙungiyar hada kan ƙungiyoyin Jama’a na Bauchi (BASNEC), Garba Jinjiri, ya bayyana irin wannan damuwa tare da bayyana rashin jin daɗin cire ƙungiyoyin jama’a daga kwamitin rabon kayan.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Wani babban jami’in Ma’aikatar Harkokin jin Kai ta Jihar Bauchi, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce har yanzu jihar ba ta samu tallafin ba, amma ya tabbatar da cewa idan an samu za a rarraba kai tsaye.

A Gombe, mazauna irinsu Mrs. Audu Alheri da Musa Ahmed sun yi ikirarin cewa ba a raba tallafin shinkafar gwamnatin tarayya ba, inda wasu ke zaton an boye kayan.

Shugaban Gombe Network of Civil Society (GONET), Yusuf Ibrahim, ya yaba da kokarin gwamnatin jihar, amma ya nemi inganta gaskiya a tsarin.

Yayin da wannan ce-ce-ku-ce ke ci gaba da faruwa, mutane suna kira ga gwamnatocin jihohin da su tabbatar tallafin ya kai ga waɗanda suka fi buƙata, tare da gudanar da tsarin rarraba tallafin cikin gaskiya da adalci.

Shinkafa
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

NYSC Ta Mayar Da Sansaninta Na Bauchi Zuwa Kwalejin Kangere 

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.