• English
  • Business News
Monday, June 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Samun Saukin Yaduwar Bakuwar Cutar Da Ta Barke A Zamfara

by Hussein Yero
1 year ago
in Labarai
0
Ana Samun Saukin Yaduwar Bakuwar Cutar Da Ta Barke A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da rashin samun cikakken rahoto a kan sanin sabuwar cutar da ta barke makwanni biyu da suka wuce a Jihar Zamfara, wadda ta yi sanadiyyar asarar rayuka; yanzu haka, ana ci gaba da samun saukin yaduwarta, wadanda kuma suka kamu da ita, na ci gaba da karbar magani a wurin da aka kebe su.

Har bayan kammala hada wannan rahoto, ana ci gaba da dakon Hukumar Kula da Yaki da Cututtuka da ke Jihar Legas da Abuja, don sanin asalin wannan cuta da ta kunno kai wannan jiha.

  • Gwamnan Zamfara Ya Ƙara Mafi Ƙarancin Albashi Daga N7,000 Zuwa N30,000, Za A Fara Biya Daga Yuni
  • Tinubu Zai Halarci Bikin Rantsar Da Mahamat Deby A Chadi

Idan za a iya tunawa dai, wannan sabuwar cuta da aka kasa sanin gabanta da bayanta, ta yi sanadiyar mutuwar mutum 13, yayin da kuma sama da mutum 500 suka kamu da ita, inda kuma rahoton bullar cutar ya tabbatar da cewa; cutar ta fi shafar yara kanana da mata a garuruwa da dama na fadin jihar ta Zamfara.

Wata majiya daga ma’aikatan lafiya ta tabbatar da cewa, a ranar Lahadin da ta gabata ne, a Kauyen Tsibiri da ke Karamar Hukumar Maradun, aka fara samun bullar wannan cuta a cikin watan Fabrairun wannan shekara da muke ciki, sannan kimanin mutum hudu sun rasa rayukansu; sakamakon kamuwa da wannan cuta, yayin da kuma mutum 228 suka kamu da cutar.

Kazalika, daga cikin wadannan mutane da suka kamu da cutar, mutum 10 sun yi matukar fuskantar matsananciyar wahala, inda aka tura su zuwa Cibiyar Yaki da Cututtuka ta Shehu Shagari da ke Gusau; babban birnin jihar, a cewar ma’aikatan lafiyar.

Labarai Masu Nasaba

Matatar Dangote Za Ta Fara Dakon Man Fetur Da Dizal Kyauta A Fadin Nijeriya

IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 

Majiyar ta kara da cewa, cutar ba wai kawai ta ci gaba da wanzuwa a tsibiri ba ne kadai, ta yadu har zuwa wasu yankunan da suka hada da Kananan Hukumomin Shinkafi, Gusau, Zurmi da kuma Karmar Hukumar Isah da ke Jihar Sokoto, wadda ta yi iyaka da Zurmi.

A Kauyen Galadi na Karamar Hukumar Shinkafi, wadanda suka kamu da cutar sun fara ne da zazzabi mai tsanani da ciwon ciki, kamar yadda wani Ma’aikacin Cibiyar Kula da Lafiya a Matakin Farko (PHC) ya bayyana.

“Mun samu rahoton fiye da mutum 100, wadanda suka kamu da cutar tare da mutuwar mutum shida, ban da kuma sauran marasa lafiya fiye da mutum 60 da aka garzaya da su zuwa manyan wuraren da aka kebe; don kula da tasu lafiyar, a cewar rahoton.

“Ko shakka babu, yaduwar wannan cuta; ta yi matukar haifar da kiraye-kiraye ga Gwamnatin Jihar Zamfara cikin gaggawa, kan bukatar karin kwararrun likitoci a wannan fage, domin shawo kan wannan sabuwar cuta da aka kasa sanin kanta kafin ta kai ga hallaka al’umma baki-daya,” in ji wani jami’in kiwon lafiya.

Musa Salisu, wani mazaunin Maradun wanda ya yi matukar kaduwa bisa barkewar wannan cuta tare kuma da jin tsoron yiwuwar fantsamar cutar zuwa wasu yankunan da ‘yan bindiga ke iko, wanda hakan zai iya haifar da tarnaki wajen kai musu agajin gaggawa.

Kwamishiniyar lafiya ta Jihar Zamfara, Dakta A’isha Anka, ta yi karin bayani a kan alamomin wannan cuta mai ban mamaki, inda ta ce; “marasa lafiya na fama da matsalar kumburin ciki, tarin, zazzabi da kuma kasala, mai yiwuwa saboda gurbataccen ruwa.

Yanzu haka dai, tuni jihar ta kai rahoton bullar cutar ga Hukumar Yaki da Cututtuka ta Nijeriya (NCDC), tare da bayar da hadin kai kan matakan da suka kamata a dauka na gaggawa.

“Mun aika da samfura zuwa dakunan gwaje-gwaje a Legas da Abuja, domin tantancewa da kuma tsara shirin shawo kan barkewar wannan cuta.

Ta kara da cewa, “mutane hudu sun rasa rayukansu, 177 kuma sun kamu da wannan sabuwar cuta da bulla a wannan jiha tamu ta Zamfara”, in ji Anka.

LEADERSHIP Hausa, ta yi kokarin jin ta bakin Jami’an Hulda da Jama’a na Ma’aikatar Lafiya ta Bello Boko, amma abin ya ci tura; inda ya bayyana cewa, sai dai a nemi, Daraktan Lafiya na Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Zamfara, Dakta Yusif Abubakar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Amurkacutar zamaniZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zamba Ba Za Ta Yaudari Al’ummomin Kasa Da Kasa Ba

Next Post

Sin: Za A Zurfafa Dangantakar Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-Tsare Tsakanin Sin Da Kenya

Related

Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba
Labarai

Matatar Dangote Za Ta Fara Dakon Man Fetur Da Dizal Kyauta A Fadin Nijeriya

57 minutes ago
IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 
Labarai

IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 

3 hours ago
Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas

5 hours ago
Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya
Manyan Labarai

Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya

14 hours ago
Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano
Labarai

Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano

17 hours ago
Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027
Manyan Labarai

Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027

19 hours ago
Next Post
Sin: Za A Zurfafa Dangantakar Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-Tsare Tsakanin Sin Da Kenya

Sin: Za A Zurfafa Dangantakar Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-Tsare Tsakanin Sin Da Kenya

LABARAI MASU NASABA

Dan Nijeriya Lookman Na Kan Gaba Wajen Lashe Kyautar Gwarzon Kwallon Kafa Na Afrika Ta Bana

Atalanta Na Neman Yuro Miliyan 50 Daga Duk Kungiyar Da Ke Son Daukar Lookman

June 16, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Matatar Dangote Za Ta Fara Dakon Man Fetur Da Dizal Kyauta A Fadin Nijeriya

June 16, 2025
IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 

IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 

June 16, 2025
Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas

Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas

June 16, 2025
Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya

Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya

June 15, 2025
Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC

Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC

June 15, 2025
PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

June 15, 2025
An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai

An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai

June 15, 2025
Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano

Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano

June 15, 2025
Dan Asalin Tudun Loess

Dan Asalin Tudun Loess

June 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.