• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Annobar Cutar Murar Tsuntsaye Ta Yadu A Jihohin Filato Da Katsina

by Abubakar Abba and Sulaiman
8 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rahotanni sun bayyana cewa, annobar cutar murar tsintsaye (Bird flu), ta bazu a Jihohin Filato da Katsina.

A makwanni biyu da suka gabata ne, Gwamnatin Tarayya ta ankarar da masu kiwo, musamman na tsintsaye da ofis-ofis na rassan likitocin dabbobi na kasar nan kan barkewar wannan cuta a Jihar Kano.

  • Badakala: Bankin Duniya Ya Kakaba Wa Kamfanoni 2 A Nijeriya Takunkumi
  • NPA Da Kamfanin NLNG Za Su Kulla Hadakar Fitar Da Iskar Gas Ketare

A ranar 23 ga watan Janairun 2025 ne, aka samu rahoton bullar cutar a yankin Farin Gada da ke Karamar Hukumar Jos ta Arewa.

Daraktan duba lafiyar dabbobi na Jihar Filato, Dakta Shase’et Sipak Dawat, a cikin sanarwar da ya fitar a jihar ya bayyana cewa, an samu barkewar annobar murar ce ga kajin gidan gona a wani wajen kiwata su, inda cutar ta harbi tsintsaye sama da 3,000.

Dakta Dawat, ya nuna damuwarsa kan yadda mai kiwon tsintsayen da cutar ta shafa ya sayar da su kafin likitocin dabbobi daga Ma’aikatar Aikin Noma da Raya Karkara su ziyarci wajen kiwon nasa, domin daukar matakan da suka dace.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

“Wannan dalili ne yasa, ake shawartar masu kiwon kajin gidan gonar da su kasance masu sanya idanu tare da tabbatar da tsaftace guraren da suke yin kiwon nasu, domin bai wa tsintsayen da suke kiwatawa kariyar da ta kamata”, in ji Dawat.

Bugu da kari, a Jihar Katsina kuwa, wani jami’in kula da lafiyar dabbobi a shiyyar Karamar Hukumar Malumfashi, Dakta Yau Ishaku; a wani sako da ya isar ga masu kiwon tsintsaye a jihar, ya bayyana bullar annonar a jihar, wanda ya sanar da cewa, ta bulla ne a cikin kwana biyu da suka wuce, kafin samun bullar ta a Jihar Filato.

“Cutar ta bulla ne a Jihar Katsina, a ranar 21 ga watan Janairun 2025, sannan kuma yana da muhimmanci ga daukacin masu kiwon tsitsayen a Kananan Hukumomin Malumfashi, Kafur da Kankara da ke karkashin ofishin shiyya a Karamar Hukumar Malumfashi, da su tabbatar da sun kiyaye wajen daukar matakai, domin kare guraren da suke aiwatar da kiwonsu daga kutsawar wannan annona.”

Ya kara da cewa, ya zama wajibi ga masu kiwon da su rika hana barin mutane suna shiga guraren da suka killace, domin kiwon nasu.

Dakta Yau, ya kuma shawarci masu kiwon da su tabbatar da suna tsaftace kayan da suke amfani da su wajen ciyar da tsitsayen da suke kiwatawa, domin kare su daga kamuwa da cututtuka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kashi 85 Na Inibin Da Ake Nomawa Nijeriya, Daga Jihar Kaduna Ne – Dalhatu

Next Post

Abubuwa Biyar Da Ya Kyautu A Mayar Da Hankali A Kansu A Kakar Noman 2025

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

1 week ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

1 week ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

3 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

3 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

1 month ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

1 month ago
Next Post
Aikin Gona

Abubuwa Biyar Da Ya Kyautu A Mayar Da Hankali A Kansu A Kakar Noman 2025

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.