ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ba Ta Da ‘Yan Takarar Sanata A Mazabun Yobe Ta Arewa Da A’Ibom Ta Arewa —INEC

by Khalid Idris Doya
4 years ago
APC

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta ce, jam’iyyar APC ba ta da ‘yan takara a kujerun ‘yan Majalisar Dattawa masu neman wakiltar mazabar Yobe ta Arewa da mazabar Akwa Ibom ta Arewa Maso Yamma.

Wadannan mazabun dai su ne wadanda aka yi ta muhawara a kansu dangane da cewa Sanata Ahmad Lawan da Godswill Akpabio sun nemi zama ‘yan takara amma kura ta tashi.

  • Zaben Fidda Gwanin PDP: Wike Ya Gurfanar Da Atiku, Tambuwal Da INEC A Gaban Kotu

Babban kwamishina kuma jami’an watsa labarai da ilmantar da masu zabe, Festus Okoye shi ne ya shaida hakan jiya a lokacin da ke magana ta cikin wani shirin gidan talabijin din Channels mai suna ‘Siyasa A Yau’ ya ce hukumar ba ta amince da kowani mutum cikin biyun a matsayin ‘yan takarar mazabun ba.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Hukumar ta fayyace komai cikin sashi na 29 subsection 1 na dokar zabe. Hakki ne na jam’iyya ta mika sunan jerin sunayen ‘yan takarar da suka samu nasara a zabukan cikin gida da aka gudanar ta sahihi kuma ingataccen hanya ga hukumar zabe ta INEC.

“Wadannan mazabun guda biyu. Sun tura wa INEC sunayen mutane biyu kuma ba mutanen da suka samu nasara ta hanyar gudanar da sahihin zaben fitar da gwani ba ne.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

“Kuma ba mu wallafa bayanansu ba, a haka ake har yanzu.”

Okoye ya ce hukumarsu ba za su fito ta je tana rokon APC ko wata jam’iyya da ta tura mata sunan wani dan takara da ya lashe zaben ta sahihin zaben cikin gida ba.

“Idan jam’iyya ba ta aiko mana da sunan wani dan takara da ya samu nasara ta sahihin zaben fitar da gwani ba, matsalar da ke akwai shine ‘ita wannan jam’iyyar’ ba ta da ‘yan takara a mazabun da hakan ya faru, kuma haka doka ta fayyace.”

Ya kara da cewa sunayen Lawan da Akpabio ne APC ta aike cikin shafin INEC inda ita kuma hukumar ta yi watsi da sunayen tare da kin amincewa da su.

“Matsalar ma shine har zuwa yanzu, APC ba ta da ‘yan takara a wadannan mazabun,” ya ce.

Ya kara da cewa ba aiki ne fitar wa jam’iyyun siyasa ‘yan takara ba, illa iyaka su sanya ido wajen gudanar da zaben fitar da gwani domin tabbatar da cewa wadanda aka tura mata sunayensu su ne suka samu nasara a zabukan cikin gida da aka gudanar ta sahihi kuma ingataccen hanya.

APC
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Ana Ci Gaba Da Samun Karuwar Wakokin Kyamar Musulmi A Indiya

Ana Ci Gaba Da Samun Karuwar Wakokin Kyamar Musulmi A Indiya

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.