• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ba Ta Da ‘Yan Takarar Sanata A Mazabun Yobe Ta Arewa Da A’Ibom Ta Arewa —INEC

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
APC Ba Ta Da ‘Yan Takarar Sanata A Mazabun Yobe Ta Arewa Da A’Ibom Ta Arewa —INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta ce, jam’iyyar APC ba ta da ‘yan takara a kujerun ‘yan Majalisar Dattawa masu neman wakiltar mazabar Yobe ta Arewa da mazabar Akwa Ibom ta Arewa Maso Yamma.

Wadannan mazabun dai su ne wadanda aka yi ta muhawara a kansu dangane da cewa Sanata Ahmad Lawan da Godswill Akpabio sun nemi zama ‘yan takara amma kura ta tashi.

  • Zaben Fidda Gwanin PDP: Wike Ya Gurfanar Da Atiku, Tambuwal Da INEC A Gaban Kotu

Babban kwamishina kuma jami’an watsa labarai da ilmantar da masu zabe, Festus Okoye shi ne ya shaida hakan jiya a lokacin da ke magana ta cikin wani shirin gidan talabijin din Channels mai suna ‘Siyasa A Yau’ ya ce hukumar ba ta amince da kowani mutum cikin biyun a matsayin ‘yan takarar mazabun ba.

Ya ce, “Hukumar ta fayyace komai cikin sashi na 29 subsection 1 na dokar zabe. Hakki ne na jam’iyya ta mika sunan jerin sunayen ‘yan takarar da suka samu nasara a zabukan cikin gida da aka gudanar ta sahihi kuma ingataccen hanya ga hukumar zabe ta INEC.

“Wadannan mazabun guda biyu. Sun tura wa INEC sunayen mutane biyu kuma ba mutanen da suka samu nasara ta hanyar gudanar da sahihin zaben fitar da gwani ba ne.

Labarai Masu Nasaba

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

“Kuma ba mu wallafa bayanansu ba, a haka ake har yanzu.”

Okoye ya ce hukumarsu ba za su fito ta je tana rokon APC ko wata jam’iyya da ta tura mata sunan wani dan takara da ya lashe zaben ta sahihin zaben cikin gida ba.

“Idan jam’iyya ba ta aiko mana da sunan wani dan takara da ya samu nasara ta sahihin zaben fitar da gwani ba, matsalar da ke akwai shine ‘ita wannan jam’iyyar’ ba ta da ‘yan takara a mazabun da hakan ya faru, kuma haka doka ta fayyace.”

Ya kara da cewa sunayen Lawan da Akpabio ne APC ta aike cikin shafin INEC inda ita kuma hukumar ta yi watsi da sunayen tare da kin amincewa da su.

“Matsalar ma shine har zuwa yanzu, APC ba ta da ‘yan takara a wadannan mazabun,” ya ce.

Ya kara da cewa ba aiki ne fitar wa jam’iyyun siyasa ‘yan takara ba, illa iyaka su sanya ido wajen gudanar da zaben fitar da gwani domin tabbatar da cewa wadanda aka tura mata sunayensu su ne suka samu nasara a zabukan cikin gida da aka gudanar ta sahihi kuma ingataccen hanya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

DA DUMI-DUMI: Ruto Ya Lashe Zaben Shugaban Kasar Kenya

Next Post

Ana Ci Gaba Da Samun Karuwar Wakokin Kyamar Musulmi A Indiya

Related

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
Labarai

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

1 hour ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

3 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

4 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

5 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

10 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

11 hours ago
Next Post
Ana Ci Gaba Da Samun Karuwar Wakokin Kyamar Musulmi A Indiya

Ana Ci Gaba Da Samun Karuwar Wakokin Kyamar Musulmi A Indiya

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.