ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ba Ta Da ‘Yan Takarar Sanata A Mazabun Yobe Ta Arewa Da A’Ibom Ta Arewa —INEC

by Khalid Idris Doya
4 years ago
APC

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta ce, jam’iyyar APC ba ta da ‘yan takara a kujerun ‘yan Majalisar Dattawa masu neman wakiltar mazabar Yobe ta Arewa da mazabar Akwa Ibom ta Arewa Maso Yamma.

Wadannan mazabun dai su ne wadanda aka yi ta muhawara a kansu dangane da cewa Sanata Ahmad Lawan da Godswill Akpabio sun nemi zama ‘yan takara amma kura ta tashi.

  • Zaben Fidda Gwanin PDP: Wike Ya Gurfanar Da Atiku, Tambuwal Da INEC A Gaban Kotu

Babban kwamishina kuma jami’an watsa labarai da ilmantar da masu zabe, Festus Okoye shi ne ya shaida hakan jiya a lokacin da ke magana ta cikin wani shirin gidan talabijin din Channels mai suna ‘Siyasa A Yau’ ya ce hukumar ba ta amince da kowani mutum cikin biyun a matsayin ‘yan takarar mazabun ba.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Hukumar ta fayyace komai cikin sashi na 29 subsection 1 na dokar zabe. Hakki ne na jam’iyya ta mika sunan jerin sunayen ‘yan takarar da suka samu nasara a zabukan cikin gida da aka gudanar ta sahihi kuma ingataccen hanya ga hukumar zabe ta INEC.

“Wadannan mazabun guda biyu. Sun tura wa INEC sunayen mutane biyu kuma ba mutanen da suka samu nasara ta hanyar gudanar da sahihin zaben fitar da gwani ba ne.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

“Kuma ba mu wallafa bayanansu ba, a haka ake har yanzu.”

Okoye ya ce hukumarsu ba za su fito ta je tana rokon APC ko wata jam’iyya da ta tura mata sunan wani dan takara da ya lashe zaben ta sahihin zaben cikin gida ba.

“Idan jam’iyya ba ta aiko mana da sunan wani dan takara da ya samu nasara ta sahihin zaben fitar da gwani ba, matsalar da ke akwai shine ‘ita wannan jam’iyyar’ ba ta da ‘yan takara a mazabun da hakan ya faru, kuma haka doka ta fayyace.”

Ya kara da cewa sunayen Lawan da Akpabio ne APC ta aike cikin shafin INEC inda ita kuma hukumar ta yi watsi da sunayen tare da kin amincewa da su.

“Matsalar ma shine har zuwa yanzu, APC ba ta da ‘yan takara a wadannan mazabun,” ya ce.

Ya kara da cewa ba aiki ne fitar wa jam’iyyun siyasa ‘yan takara ba, illa iyaka su sanya ido wajen gudanar da zaben fitar da gwani domin tabbatar da cewa wadanda aka tura mata sunayensu su ne suka samu nasara a zabukan cikin gida da aka gudanar ta sahihi kuma ingataccen hanya.

APC
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
Ana Ci Gaba Da Samun Karuwar Wakokin Kyamar Musulmi A Indiya

Ana Ci Gaba Da Samun Karuwar Wakokin Kyamar Musulmi A Indiya

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.