ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Fidda Gwanin PDP: Wike Ya Gurfanar Da Atiku, Tambuwal Da INEC A Gaban Kotu

Yana fatan a bata masa kuri'un dan takarar PDP don cikar burinsa.

by Muhammad
4 years ago
Zaben

Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya maka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, a gaban wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, kan tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a 2023.

A cikin karar, Gwamna Wike, da wani jigo a PDP da kuma wani, Michael Ekamon, an lissafo su a matsayin masu shigar da kara bi da bi.

  • Rikicin PDP: Ba Za Mu Bai Wa Wadanda Ba Sa Kaunar Ribas Kuri’unmu Ba – Wike
  • Me Ya Sa Ake Rubibin Wike A Siyasar Nijeriya?

Sauran wadanda ake tuhumar sun hada da Gwamna Aminu Tambuwal na jihar Sokoto da kuma hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).

ADVERTISEMENT

A cewar bayanan kotun, an yi amfani da dukkan matakai akan dukkan bangarorin da ke cikin lamarin.

Wike ya roki kotun da ta duba yuyuwar tsige Tambuwal ya daga mukaminsa saboda rashin sauka daga kujerarsa lokacin zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar PDP ko kuma ya rasa kuri’unsa.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Wike da Ekamon sun yi zargin cewa idan har za a tantance batutuwan da suka dace, kotu ta ba da sassauci har guda tara da suka hada da bayyana cewa za a soke zaben Tambuwal na kuri’un Atiku.

Masu shigar da karar sun kuma nemi a bayyana cewa PDP ta yi sakaci da rashin tausayi ta hanyar baiwa Atiku kuri’un gwamnan jihar Sokoto a zaben fidda gwani da aka gudanar a babban taron jam’iyyar PDP na kasa a watan Mayu, 2022.

Sun roki kotun da ta soke zaben da kuma umarnin da ya hana wanda ake kara na 3 (Tambuwal) janyewa a zaben fidda gwani bayan an fara kada kuri’a.

Masu neman takarar sun kuma roki kotun da ta bayyana cewa PDP da Atiku sun yi amfani da damar da ba ta dace ba wajen janyewar Tambuwal a lokacin da suka baiwa gwamnan Sokoto damar neman kuri’un wakilai masu zabe da su zabi tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku a wannan zaben.

Wike da Ekamon sun roki kotun da ta umurci INEC da ta ki amincewa ko ta cire Atiku daga cikin ‘yan takararta a zaben shugaban kasa na 2023.

Suna kuma neman kotun da ta bayar da umurnin jam’iyyar PDP da ta sake kidaya kuri’un zaben fidda gwani da aka gudanar a ranakun Asabar 28 ga watan Mayu da kuma Lahadi 29 ga watan Mayun 2022.

Zaben
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Labarin Asadulmuluuk (36)

Labarin Asadulmuluuk (36)

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.