• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ta Lalata Nijeriya, PDP Kuma Matacciyar Jam’iyya Ce — Kwankwaso

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
7 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
APC Ta Lalata Nijeriya, PDP Kuma Matacciyar Jam’iyya Ce — Kwankwaso
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon gwamnan Jihar Kano, kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya caccaki jam’iyyar APC mai mulki a karkashin Shugaban kasa Bola Tinubu, inda ya bayyana cewa manufofinta sun kara ta’azzara talauci da yunwa da kuma karuwar rashin tsaro.

 

Kwankwaso, wanda ya bayyana haka a taron kwamitin zartarwa na kasa karo na 7 na jam’iyyar NNPP a Abuja ranar Litinin, ya kuma bayyana PDP a matsayin matacciyar jam’iyyar da ke fama da rikicin cikin gida d take fuskanta a halin yanzu.

  • Kasashe Fiye Da Dari Sun Ki Yarda Da Siyasantar Da Batun Hakkin Dan Adam 
  • Sin Ta Bukaci Kwamitin Sulhun MDD Da Ya Ingiza Sassauta Rikicin Lebanon Da Isra’ila

Yayin da yake bayyana NNPP a matsayin jam’iyyar da ta fi kowace jam’iyya tabaka a Nijeriya, ya ce ita ce jam’iyya daya tilo da za ta iya samar da shugabanci na gaskiya da zai magance bukatun ‘yan Nijeriya da kuma kawo musu dauki.

 

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

“Jam’iyyarmu tana aiki tukuru wajen ganin yadda za mu ingnta shugabancin da kowa zai gamsu da shi domin ci gabanmu.

 

“Tabbas muna samun hassada a wajen jam’iyyarmu tare da kai mana farmaki daga ciki da ma wajen jam’iyyarmu.

 

“Na yi matukar farin ciki duk da irin kalubalen da muke fuskanta, a yau jam’iyyarmu, ita ce jam’iyya mafi habaka a kasar nan.

 

“Na tuna lokacin da na ziyarci Katsina domin bude ofishinmu na jihar, a can na bayyana cewa jam’iyyun nan guda biyu, wato APC da PDP, musamman jam’iyyar PDP ta mutu kuma akwai matsaloli masu tarin yawa a cikin jam’iyyar.

 

“Na tabbata a lokacin da nake wannan furuci, da yawa daga cikinsu sun ga abin da ke faruwa a yau, wanda ake kokarin yi wa jam’iyyar gunduwa-gunduwa, jam’iyyar na cikin babbar matsala, don haka idan ba su fahimci wancan lokacin ba, to yanzu ina ganin sun fahimta kuma za su amince da abun da muke fada cewa jam’iyyar ta mutu.

 

“Jam’iyyar APC kamar yadda take a yau, za ka ga cewa ita ke shugabanci a sama, amma kuma al’ummar kasar nan gaba daya sun samu koma-baya.

 

“A wannan matakin ko sun yarda cewa suna yin kokari amma dukkanmu, musamman masu kada kuri’a a kasar nan mun yi imanin cewa ba su tabuka abin kirki ba, musamman idan aka yi la’akari da batun tsaro, talauci a kasar nan da kuma matsalar yunwa da muke gani a Nijeriya.

 

“Don haka, mun gode wa Allah da cewa jam’iyyun biyu duk sun durkushe, jam’iyyarmu ta NNPP tana habaka. Mun gode wa Allah Madaukakin Sarki a kan haka,” in ji Kwankwaso.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kirkirar Kimiyya Da Fasaha Ta Kasar Sin Na Sa Kaimi Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Next Post

Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

2 weeks ago
Kwankwaso
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

2 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

2 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

3 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

3 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

3 weeks ago
Next Post
Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya

Shekara 64 Da Samun 'Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi - 'Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.