ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ta Lalata Nijeriya, PDP Kuma Matacciyar Jam’iyya Ce — Kwankwaso

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
1 year ago
Kwankwaso

Tsohon gwamnan Jihar Kano, kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya caccaki jam’iyyar APC mai mulki a karkashin Shugaban kasa Bola Tinubu, inda ya bayyana cewa manufofinta sun kara ta’azzara talauci da yunwa da kuma karuwar rashin tsaro.

 

Kwankwaso, wanda ya bayyana haka a taron kwamitin zartarwa na kasa karo na 7 na jam’iyyar NNPP a Abuja ranar Litinin, ya kuma bayyana PDP a matsayin matacciyar jam’iyyar da ke fama da rikicin cikin gida d take fuskanta a halin yanzu.

ADVERTISEMENT
  • Kasashe Fiye Da Dari Sun Ki Yarda Da Siyasantar Da Batun Hakkin Dan Adam 
  • Sin Ta Bukaci Kwamitin Sulhun MDD Da Ya Ingiza Sassauta Rikicin Lebanon Da Isra’ila

Yayin da yake bayyana NNPP a matsayin jam’iyyar da ta fi kowace jam’iyya tabaka a Nijeriya, ya ce ita ce jam’iyya daya tilo da za ta iya samar da shugabanci na gaskiya da zai magance bukatun ‘yan Nijeriya da kuma kawo musu dauki.

 

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

“Jam’iyyarmu tana aiki tukuru wajen ganin yadda za mu ingnta shugabancin da kowa zai gamsu da shi domin ci gabanmu.

 

“Tabbas muna samun hassada a wajen jam’iyyarmu tare da kai mana farmaki daga ciki da ma wajen jam’iyyarmu.

 

“Na yi matukar farin ciki duk da irin kalubalen da muke fuskanta, a yau jam’iyyarmu, ita ce jam’iyya mafi habaka a kasar nan.

 

“Na tuna lokacin da na ziyarci Katsina domin bude ofishinmu na jihar, a can na bayyana cewa jam’iyyun nan guda biyu, wato APC da PDP, musamman jam’iyyar PDP ta mutu kuma akwai matsaloli masu tarin yawa a cikin jam’iyyar.

 

“Na tabbata a lokacin da nake wannan furuci, da yawa daga cikinsu sun ga abin da ke faruwa a yau, wanda ake kokarin yi wa jam’iyyar gunduwa-gunduwa, jam’iyyar na cikin babbar matsala, don haka idan ba su fahimci wancan lokacin ba, to yanzu ina ganin sun fahimta kuma za su amince da abun da muke fada cewa jam’iyyar ta mutu.

 

“Jam’iyyar APC kamar yadda take a yau, za ka ga cewa ita ke shugabanci a sama, amma kuma al’ummar kasar nan gaba daya sun samu koma-baya.

 

“A wannan matakin ko sun yarda cewa suna yin kokari amma dukkanmu, musamman masu kada kuri’a a kasar nan mun yi imanin cewa ba su tabuka abin kirki ba, musamman idan aka yi la’akari da batun tsaro, talauci a kasar nan da kuma matsalar yunwa da muke gani a Nijeriya.

 

“Don haka, mun gode wa Allah da cewa jam’iyyun biyu duk sun durkushe, jam’iyyarmu ta NNPP tana habaka. Mun gode wa Allah Madaukakin Sarki a kan haka,” in ji Kwankwaso.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

November 14, 2025
Tambarin Dimokuradiyya

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

November 14, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Next Post
Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya

Shekara 64 Da Samun 'Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi - 'Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

November 17, 2025
Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025
Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

November 17, 2025
Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

November 17, 2025
Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.