• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APOSUN Ta Lashi Takobin Tsaftace Sana’ar POS A Fadin Kasar Nan

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
in Labarai
0
APOSUN Ta Lashi Takobin Tsaftace Sana’ar POS A Fadin Kasar Nan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar masu rajin tsaftace sana’ar POS ta Nijeriya (APOSUN), ta jaddada kudirinta na yaki da zamba da sauran haramtattun kudade da masu sana’ar na cikin mambobinta a fadin kasar nan.

Shugaban Kwamitin Amintattun Kungiyar na Kasa, Barista Ibrahim Abdullahi, shi ya bayyana hakan a lokacin da suka kai ziyarar ban girma ga wasu masu ruwa da tsaki a Babban Birnin Tarayya Abuja.

  • SCMP: Amurka Za Ta Iya Fadawa Rikici Sakamakon Mummunar Manufarta Ta Neman Dakile Cigaban Sin

Ya kara da cewa dalilin da ya sa suka kai ziyarar shi ne, domin sanar da cibiyoyin gargajiya da sauran masu hannu da shuni kan yadda za su inganta sana’arsu ta POS a Babban Birnin Tarayya da ma kasa baki daya.

Shugaban kwamitin ya kara da cewa matakin zai kuma taimaka wajen samun ci gaban tsaro tare da fadakar da mambobinsu kan shugabannin babban bankin Nijeriya (CBN).

“Ko ina aka bi a kasar nan lungu da sako za ka samu akwai mambobinmu masu gudanar da wannan sana’a ta POS, don haka ne muka lashi takobin ganin mun tsaftace sana’ar domin kaucewa yawan almundahana, zamba, damfara da sauran abubuwa na zalunci da suka addabar masu sana’ar da kuma masu zuwa domin yin mu’amala da su.

Labarai Masu Nasaba

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

“Mun sani cewa kowace sana’a akwai mutanen kirki da kuma mutanen kawai, domin sau da yawa za ka samu wasu suna korafi kan masu gudanar da sana’ar wasu kuma masu sana’ar ne suke korafi kan masu zuwa domin mu’amala da su, in ji shi.

Don haka ya ce ya zama wajibi ga kowane mai wannan sana’a ya zama ya yi rajista domin ta haka ne za a tantance masu gaskiya da kuma marasa gaskiya, sannan kuma hakan zai taimaka wa jami’an tsaro wajen dakile haramtattun harkoki da ake yi na aika wa da kudaden fansa ga masu garkuwa da mutane.

Da yake mayar da martani kan ziyarar, Shugaban Majalisar Masarautun Abuja wanda shi ne Sarkin Abaji, Dakta Adamu Baba Yunusa ya nuna jin dadinsa ga kungiyar yadda ta bayyana su a matsayin daya daga cikin masu kokarin ganin sun tsaftace wannan sana’a ta POS, inda ya jaddada cewa za su ci gaba da mai da hankali kan yaki da zamba da almyndahana sauran haramtattun ayyuka da za su iya shafar mutucin ‘yan Nijeriya.
Sarkin na Abaji ya kuma bukaci kungiyar da ta fara horar da ‘ya’yanta domin a cewarsa hakan zai inganta kwarewarsu tare da yin gogayya da sauran masu gudanar da harkar POS a kasashen duniya.

Ya kuma yi kira gare su da su sake mai da hankali kan aikin da suka dauko domin aiki ne ja wanda dole sai sun yi tsayin daka a kansa.

“Wannan fa aki ne ja a gabanku, yanzu ya zama dole a kanku ku rika shirya taruka na wayar da kan jama’a domin wasu na shiga sana’ar ce ba tare da ilimi ba, don haka a ke ta samun korafe-korafe, ta yadda zai zama sun cuci abokin huldarsu ko shi ya cuce su, wannan duk rashin ilim ne. Don haka wannan aiki ne a gabanku na koyar da mambobinku yadda sana’ar za ta dore a samu nasara, duk abin da babu ilimi a ciknsa to lallai za a yi ta samun matsala.

“Mu kuma za mu yi abin da za mu iya na ganain mun wayar da kan jama’armu domin abin da kuka zo da shi abu ne na alheri sam barka. Ina yi muku addu’a da fatan Allah ya yi riko da hannayenku ya baku nasara,” in ji shi.

A wata ziyarar makamanciyarta da suka kai wa Daraktan Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS), na Abuja, Ado Mu’azu ya tabbatar da shirinsu na yaki da zamba da almundahana, inda ya basu tabbacin goyon baya da hadin kai.

Kazalika Daraktan ya nuna farin cikinsa da samuwar wannan kungiya, inda ya ce babu shakka ya hakan zai yi tasirin sosai wajen rage zaman banza gami da sama wa matasa abin yi, sannan ya ja hankalin mambobin kungiyar da zama masu jajircewa da hakuri kan ayyukan da suka sa a gaba.

A karshe ya yaba wa shugabannin kungiyar bisa zurfin tunaninsu na samar da kungiyar, sannan kuma ya yi fatan alheri gare su da addu’ar samun nasara kan wannan ai ki da suka sa a gaba.

A halin da ake ciki kungiyar masu amfani da na’urar ta POS a Nijeriya APOSUN ta yi kira ga jama’a da su ba da hadin kai ga mambobinsu a fadin jihohi domin samar da ayyukan yi da kuma ci gaban tattalin arzikin kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NIS Reshen Bayelsa Ta Horas Da Jami’anta A Kan Kyautata Rayuwarsu

Next Post

An Kaddamar Da Alkur’ani Da Aka Fassara Zuwa Harshen Igbo A Abuja

Related

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace
Manyan Labarai

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

1 hour ago
‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

2 hours ago
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal
Labarai

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

16 hours ago
Kotu Ta Yanke Wa ÆŠan TikTok Tsulange Hukuncin ÆŠauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci
Labarai

Kotu Ta Yanke Wa ÆŠan TikTok Tsulange Hukuncin ÆŠauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

16 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku

17 hours ago
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Ra'ayi Riga

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

18 hours ago
Next Post
An Kaddamar Da Alkur’ani Da Aka Fassara Zuwa Harshen Igbo A Abuja

An Kaddamar Da Alkur'ani Da Aka Fassara Zuwa Harshen Igbo A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

July 4, 2025
‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

July 4, 2025
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Kungiyar MEMAN Ta Yi Maraba Da Shirin Dangote Na Rabar Da Man Fetur

July 4, 2025
NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku

NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku

July 4, 2025
Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.