ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APOSUN Ta Lashi Takobin Tsaftace Sana’ar POS A Fadin Kasar Nan

by Rabi'u Ali Indabawa
4 years ago
POS

Kungiyar masu rajin tsaftace sana’ar POS ta Nijeriya (APOSUN), ta jaddada kudirinta na yaki da zamba da sauran haramtattun kudade da masu sana’ar na cikin mambobinta a fadin kasar nan.

Shugaban Kwamitin Amintattun Kungiyar na Kasa, Barista Ibrahim Abdullahi, shi ya bayyana hakan a lokacin da suka kai ziyarar ban girma ga wasu masu ruwa da tsaki a Babban Birnin Tarayya Abuja.

  • SCMP: Amurka Za Ta Iya Fadawa Rikici Sakamakon Mummunar Manufarta Ta Neman Dakile Cigaban Sin

Ya kara da cewa dalilin da ya sa suka kai ziyarar shi ne, domin sanar da cibiyoyin gargajiya da sauran masu hannu da shuni kan yadda za su inganta sana’arsu ta POS a Babban Birnin Tarayya da ma kasa baki daya.

ADVERTISEMENT

Shugaban kwamitin ya kara da cewa matakin zai kuma taimaka wajen samun ci gaban tsaro tare da fadakar da mambobinsu kan shugabannin babban bankin Nijeriya (CBN).

“Ko ina aka bi a kasar nan lungu da sako za ka samu akwai mambobinmu masu gudanar da wannan sana’a ta POS, don haka ne muka lashi takobin ganin mun tsaftace sana’ar domin kaucewa yawan almundahana, zamba, damfara da sauran abubuwa na zalunci da suka addabar masu sana’ar da kuma masu zuwa domin yin mu’amala da su.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

“Mun sani cewa kowace sana’a akwai mutanen kirki da kuma mutanen kawai, domin sau da yawa za ka samu wasu suna korafi kan masu gudanar da sana’ar wasu kuma masu sana’ar ne suke korafi kan masu zuwa domin mu’amala da su, in ji shi.

Don haka ya ce ya zama wajibi ga kowane mai wannan sana’a ya zama ya yi rajista domin ta haka ne za a tantance masu gaskiya da kuma marasa gaskiya, sannan kuma hakan zai taimaka wa jami’an tsaro wajen dakile haramtattun harkoki da ake yi na aika wa da kudaden fansa ga masu garkuwa da mutane.

Da yake mayar da martani kan ziyarar, Shugaban Majalisar Masarautun Abuja wanda shi ne Sarkin Abaji, Dakta Adamu Baba Yunusa ya nuna jin dadinsa ga kungiyar yadda ta bayyana su a matsayin daya daga cikin masu kokarin ganin sun tsaftace wannan sana’a ta POS, inda ya jaddada cewa za su ci gaba da mai da hankali kan yaki da zamba da almyndahana sauran haramtattun ayyuka da za su iya shafar mutucin ‘yan Nijeriya.
Sarkin na Abaji ya kuma bukaci kungiyar da ta fara horar da ‘ya’yanta domin a cewarsa hakan zai inganta kwarewarsu tare da yin gogayya da sauran masu gudanar da harkar POS a kasashen duniya.

Ya kuma yi kira gare su da su sake mai da hankali kan aikin da suka dauko domin aiki ne ja wanda dole sai sun yi tsayin daka a kansa.

“Wannan fa aki ne ja a gabanku, yanzu ya zama dole a kanku ku rika shirya taruka na wayar da kan jama’a domin wasu na shiga sana’ar ce ba tare da ilimi ba, don haka a ke ta samun korafe-korafe, ta yadda zai zama sun cuci abokin huldarsu ko shi ya cuce su, wannan duk rashin ilim ne. Don haka wannan aiki ne a gabanku na koyar da mambobinku yadda sana’ar za ta dore a samu nasara, duk abin da babu ilimi a ciknsa to lallai za a yi ta samun matsala.

“Mu kuma za mu yi abin da za mu iya na ganain mun wayar da kan jama’armu domin abin da kuka zo da shi abu ne na alheri sam barka. Ina yi muku addu’a da fatan Allah ya yi riko da hannayenku ya baku nasara,” in ji shi.

A wata ziyarar makamanciyarta da suka kai wa Daraktan Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS), na Abuja, Ado Mu’azu ya tabbatar da shirinsu na yaki da zamba da almundahana, inda ya basu tabbacin goyon baya da hadin kai.

Kazalika Daraktan ya nuna farin cikinsa da samuwar wannan kungiya, inda ya ce babu shakka ya hakan zai yi tasirin sosai wajen rage zaman banza gami da sama wa matasa abin yi, sannan ya ja hankalin mambobin kungiyar da zama masu jajircewa da hakuri kan ayyukan da suka sa a gaba.

A karshe ya yaba wa shugabannin kungiyar bisa zurfin tunaninsu na samar da kungiyar, sannan kuma ya yi fatan alheri gare su da addu’ar samun nasara kan wannan ai ki da suka sa a gaba.

A halin da ake ciki kungiyar masu amfani da na’urar ta POS a Nijeriya APOSUN ta yi kira ga jama’a da su ba da hadin kai ga mambobinsu a fadin jihohi domin samar da ayyukan yi da kuma ci gaban tattalin arzikin kasa.

POS
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
An Kaddamar Da Alkur’ani Da Aka Fassara Zuwa Harshen Igbo A Abuja

An Kaddamar Da Alkur'ani Da Aka Fassara Zuwa Harshen Igbo A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.