• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asalin Abin Da Ya Faru Game Da Dawowar ‘Yan Bindiga Hanyar Kaduna Zuwa Abuja – ‘Yansanda

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Abuja

‘Yansanda sun tabbatar da cewa mutane shida ne suka jikkata a wata arangama tsakanin jami’an tsaro da ‘yan bindiga a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja.

Rundunar ‘yansandan ta ce lamarin ya faru ne a ranar 6 ga watan Janairu, 2024, lokacin da wasu gungun ‘yan bindiga suka yi yunkurin tsallaka babban titin, inda jami’an tsaro suka afka musu domin tarwatsa su.

  • Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Shekarar 2023
  • Nijeriya Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Aikin Hajjin 2024

A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na Rundunar ‘yansandan jihar Kaduna, ASP Mansur Hassan, ya fitar, rundunar ta yi karin haske kan lamarin domin warware zare da abawa a kan wani rahoto da aka bayar na sace mutane a wannan ranar a kusa da Kateri.

Kwamishinan ‘yansanda na jihar, Audu Ali ya bukaci ‘yan jarida da su rika tantance bayanai daga hukumomin tsaro da sauran wadanda abin ya shafa kafin su wallafa.

A ranar Talatar makon nan, daya daga cikin jaridun kasar nan ta ruwaito cewa an sace matafiya a kusa da kauyen Kateri a wani samame na tsawon mintuna 45 da ‘yan bindiga suka kai a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja, a ranar Lahadi tare da sace mutum 30.

LABARAI MASU NASABA

Wani Sabon Hari Kan Al’ummar Da Ke Iyaka Da Katsina A Kano Ya Rutsa Da Mata 5

Yadda Sojoji Suka Tarwatsa Haramtattun Matatun Mai 14 A Yankin Neja Delta 

Rundunar ta jaddada bukatar ‘yan jarida su rika tantance gaskiyar bayanan da suke samu a wurin jami’an tsaro kafin su kai ga bugawa.

Rundunar ‘yansandan ta ce lamarin ya faru ne a kusa da wani wuri da ake kira da Dogon Fili, kuma a yayin musayar wuta ne mutane shida suka ji raunuka daban-daban da harsasai.

“Wadanda suka jikkata sun hada da Jibrin Tasiu, Jummai Abubakar, Zafira Abubakar, AbdulKarim Nurudeen, L/Cpl Chinedu Jerry Moneke, da Ayo James. Ba tare da bata lokaci ba an kai su asibiti domin kula da lafiyarsu,” in ji ‘yansandan.

Rundunar ‘yansandan ta yi kira ga al’ummar yankin da abin ya shafa da su kai rahoton duk mutumin da ake zargin ya ji rauni sakamakon harbin bindiga ga ofishin ‘yansanda mafi kusa da su.

Rundunar ta jadadda cewa abin da ya faru na da matukar ban takaici amma ta jaddada cewa a halin yanzu an kawar da barazanar da ke hanyar, matafiya na iya ci gaba da kai-komonsu lami lafiya.

Jaridar da ta bayar da labarin dai ta ce wannan ne karon farko da ‘yan bindigar suka kawo hari a hanyar ta Kaduna zuwa Abuja cikin watanni 10.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo
Labarai

Wani Sabon Hari Kan Al’ummar Da Ke Iyaka Da Katsina A Kano Ya Rutsa Da Mata 5

November 10, 2025
Matatun mai
Labarai

Yadda Sojoji Suka Tarwatsa Haramtattun Matatun Mai 14 A Yankin Neja Delta 

November 10, 2025
Jibrin Kofa
Labarai

Ɗan Majalisar Wakilai, Jibrin Ƙofa Ya Sauya Sheƙa Daga NNPP Zuwa APC

November 10, 2025
Next Post
Za A Kulle Miliyoyin Asusun Banki Saboda Rashin Katin Dan Kasa

Za A Kulle Miliyoyin Asusun Banki Saboda Rashin Katin Dan Kasa

LABARAI MASU NASABA

Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

Wani Sabon Hari Kan Al’ummar Da Ke Iyaka Da Katsina A Kano Ya Rutsa Da Mata 5

November 10, 2025
Matatun mai

Yadda Sojoji Suka Tarwatsa Haramtattun Matatun Mai 14 A Yankin Neja Delta 

November 10, 2025
Jibrin Kofa

Ɗan Majalisar Wakilai, Jibrin Ƙofa Ya Sauya Sheƙa Daga NNPP Zuwa APC

November 10, 2025
Boko haram

Sojoji Sun Fatattaki Boko Haram, Sun Ceto Mutane 86 Da Aka Sace A Borno

November 10, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.