• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asalin Abin Da Ya Faru Game Da Dawowar ‘Yan Bindiga Hanyar Kaduna Zuwa Abuja – ‘Yansanda

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
Asalin Abin Da Ya Faru Game Da Dawowar ‘Yan Bindiga Hanyar Kaduna Zuwa Abuja – ‘Yansanda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yansanda sun tabbatar da cewa mutane shida ne suka jikkata a wata arangama tsakanin jami’an tsaro da ‘yan bindiga a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja.

Rundunar ‘yansandan ta ce lamarin ya faru ne a ranar 6 ga watan Janairu, 2024, lokacin da wasu gungun ‘yan bindiga suka yi yunkurin tsallaka babban titin, inda jami’an tsaro suka afka musu domin tarwatsa su.

  • Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Shekarar 2023
  • Nijeriya Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Aikin Hajjin 2024

A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na Rundunar ‘yansandan jihar Kaduna, ASP Mansur Hassan, ya fitar, rundunar ta yi karin haske kan lamarin domin warware zare da abawa a kan wani rahoto da aka bayar na sace mutane a wannan ranar a kusa da Kateri.

Kwamishinan ‘yansanda na jihar, Audu Ali ya bukaci ‘yan jarida da su rika tantance bayanai daga hukumomin tsaro da sauran wadanda abin ya shafa kafin su wallafa.

A ranar Talatar makon nan, daya daga cikin jaridun kasar nan ta ruwaito cewa an sace matafiya a kusa da kauyen Kateri a wani samame na tsawon mintuna 45 da ‘yan bindiga suka kai a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja, a ranar Lahadi tare da sace mutum 30.

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Rundunar ta jaddada bukatar ‘yan jarida su rika tantance gaskiyar bayanan da suke samu a wurin jami’an tsaro kafin su kai ga bugawa.

Rundunar ‘yansandan ta ce lamarin ya faru ne a kusa da wani wuri da ake kira da Dogon Fili, kuma a yayin musayar wuta ne mutane shida suka ji raunuka daban-daban da harsasai.

“Wadanda suka jikkata sun hada da Jibrin Tasiu, Jummai Abubakar, Zafira Abubakar, AbdulKarim Nurudeen, L/Cpl Chinedu Jerry Moneke, da Ayo James. Ba tare da bata lokaci ba an kai su asibiti domin kula da lafiyarsu,” in ji ‘yansandan.

Rundunar ‘yansandan ta yi kira ga al’ummar yankin da abin ya shafa da su kai rahoton duk mutumin da ake zargin ya ji rauni sakamakon harbin bindiga ga ofishin ‘yansanda mafi kusa da su.

Rundunar ta jadadda cewa abin da ya faru na da matukar ban takaici amma ta jaddada cewa a halin yanzu an kawar da barazanar da ke hanyar, matafiya na iya ci gaba da kai-komonsu lami lafiya.

Jaridar da ta bayar da labarin dai ta ce wannan ne karon farko da ‘yan bindigar suka kawo hari a hanyar ta Kaduna zuwa Abuja cikin watanni 10.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hanyar AbujaMasu GarkuwaYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sau Daya Tak Gwamnati Ta Biya Karin Albashi Na N35, 000 – TUC

Next Post

Za A Kulle Miliyoyin Asusun Banki Saboda Rashin Katin Dan Kasa

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

4 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

4 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

5 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

5 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

8 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

9 hours ago
Next Post
Za A Kulle Miliyoyin Asusun Banki Saboda Rashin Katin Dan Kasa

Za A Kulle Miliyoyin Asusun Banki Saboda Rashin Katin Dan Kasa

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.