ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asalin Abin Da Ya Faru Game Da Dawowar ‘Yan Bindiga Hanyar Kaduna Zuwa Abuja – ‘Yansanda

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Abuja

‘Yansanda sun tabbatar da cewa mutane shida ne suka jikkata a wata arangama tsakanin jami’an tsaro da ‘yan bindiga a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja.

Rundunar ‘yansandan ta ce lamarin ya faru ne a ranar 6 ga watan Janairu, 2024, lokacin da wasu gungun ‘yan bindiga suka yi yunkurin tsallaka babban titin, inda jami’an tsaro suka afka musu domin tarwatsa su.

  • Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Shekarar 2023
  • Nijeriya Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Aikin Hajjin 2024

A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na Rundunar ‘yansandan jihar Kaduna, ASP Mansur Hassan, ya fitar, rundunar ta yi karin haske kan lamarin domin warware zare da abawa a kan wani rahoto da aka bayar na sace mutane a wannan ranar a kusa da Kateri.

ADVERTISEMENT

Kwamishinan ‘yansanda na jihar, Audu Ali ya bukaci ‘yan jarida da su rika tantance bayanai daga hukumomin tsaro da sauran wadanda abin ya shafa kafin su wallafa.

A ranar Talatar makon nan, daya daga cikin jaridun kasar nan ta ruwaito cewa an sace matafiya a kusa da kauyen Kateri a wani samame na tsawon mintuna 45 da ‘yan bindiga suka kai a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja, a ranar Lahadi tare da sace mutum 30.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Rundunar ta jaddada bukatar ‘yan jarida su rika tantance gaskiyar bayanan da suke samu a wurin jami’an tsaro kafin su kai ga bugawa.

Rundunar ‘yansandan ta ce lamarin ya faru ne a kusa da wani wuri da ake kira da Dogon Fili, kuma a yayin musayar wuta ne mutane shida suka ji raunuka daban-daban da harsasai.

“Wadanda suka jikkata sun hada da Jibrin Tasiu, Jummai Abubakar, Zafira Abubakar, AbdulKarim Nurudeen, L/Cpl Chinedu Jerry Moneke, da Ayo James. Ba tare da bata lokaci ba an kai su asibiti domin kula da lafiyarsu,” in ji ‘yansandan.

Rundunar ‘yansandan ta yi kira ga al’ummar yankin da abin ya shafa da su kai rahoton duk mutumin da ake zargin ya ji rauni sakamakon harbin bindiga ga ofishin ‘yansanda mafi kusa da su.

Rundunar ta jadadda cewa abin da ya faru na da matukar ban takaici amma ta jaddada cewa a halin yanzu an kawar da barazanar da ke hanyar, matafiya na iya ci gaba da kai-komonsu lami lafiya.

Jaridar da ta bayar da labarin dai ta ce wannan ne karon farko da ‘yan bindigar suka kawo hari a hanyar ta Kaduna zuwa Abuja cikin watanni 10.

Abuja
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
Za A Kulle Miliyoyin Asusun Banki Saboda Rashin Katin Dan Kasa

Za A Kulle Miliyoyin Asusun Banki Saboda Rashin Katin Dan Kasa

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.