ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asalin Abin Da Ya Faru Game Da Dawowar ‘Yan Bindiga Hanyar Kaduna Zuwa Abuja – ‘Yansanda

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Abuja

‘Yansanda sun tabbatar da cewa mutane shida ne suka jikkata a wata arangama tsakanin jami’an tsaro da ‘yan bindiga a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja.

Rundunar ‘yansandan ta ce lamarin ya faru ne a ranar 6 ga watan Janairu, 2024, lokacin da wasu gungun ‘yan bindiga suka yi yunkurin tsallaka babban titin, inda jami’an tsaro suka afka musu domin tarwatsa su.

  • Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Shekarar 2023
  • Nijeriya Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Aikin Hajjin 2024

A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na Rundunar ‘yansandan jihar Kaduna, ASP Mansur Hassan, ya fitar, rundunar ta yi karin haske kan lamarin domin warware zare da abawa a kan wani rahoto da aka bayar na sace mutane a wannan ranar a kusa da Kateri.

ADVERTISEMENT

Kwamishinan ‘yansanda na jihar, Audu Ali ya bukaci ‘yan jarida da su rika tantance bayanai daga hukumomin tsaro da sauran wadanda abin ya shafa kafin su wallafa.

A ranar Talatar makon nan, daya daga cikin jaridun kasar nan ta ruwaito cewa an sace matafiya a kusa da kauyen Kateri a wani samame na tsawon mintuna 45 da ‘yan bindiga suka kai a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja, a ranar Lahadi tare da sace mutum 30.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Rundunar ta jaddada bukatar ‘yan jarida su rika tantance gaskiyar bayanan da suke samu a wurin jami’an tsaro kafin su kai ga bugawa.

Rundunar ‘yansandan ta ce lamarin ya faru ne a kusa da wani wuri da ake kira da Dogon Fili, kuma a yayin musayar wuta ne mutane shida suka ji raunuka daban-daban da harsasai.

“Wadanda suka jikkata sun hada da Jibrin Tasiu, Jummai Abubakar, Zafira Abubakar, AbdulKarim Nurudeen, L/Cpl Chinedu Jerry Moneke, da Ayo James. Ba tare da bata lokaci ba an kai su asibiti domin kula da lafiyarsu,” in ji ‘yansandan.

Rundunar ‘yansandan ta yi kira ga al’ummar yankin da abin ya shafa da su kai rahoton duk mutumin da ake zargin ya ji rauni sakamakon harbin bindiga ga ofishin ‘yansanda mafi kusa da su.

Rundunar ta jadadda cewa abin da ya faru na da matukar ban takaici amma ta jaddada cewa a halin yanzu an kawar da barazanar da ke hanyar, matafiya na iya ci gaba da kai-komonsu lami lafiya.

Jaridar da ta bayar da labarin dai ta ce wannan ne karon farko da ‘yan bindigar suka kawo hari a hanyar ta Kaduna zuwa Abuja cikin watanni 10.

Abuja
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Za A Kulle Miliyoyin Asusun Banki Saboda Rashin Katin Dan Kasa

Za A Kulle Miliyoyin Asusun Banki Saboda Rashin Katin Dan Kasa

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.