• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ASUU Ta Fara Gangamin Shiga Yajin Aiki Yayin Da Gwamnatin Tarayya Ta Kasa Cika Alkawari

by Idris Aliyu Daudawa
7 months ago
in Ilimi, Kasashen Ketare
0
ASUU Ta Fara Gangamin Shiga Yajin Aiki Yayin Da Gwamnatin Tarayya Ta Kasa Cika Alkawari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da akwai alamun jami’oi za su fara wani yajin aikin da za s a al’amuran koyarwa su tsaya, yayin da gwamnatin tarayya ta kasa cika alkawarin yarjejeniyar da ta sa hannu da kungiyar Malaman jami’oi ta kasa (ASUU).

Jaridar Guardian ta bada rahoton cewa kungiyar ta damu kwarai kan rashin cika alkawarin da gwamnatin tarayya ta yi da ita, na samar da Naira bilyan 200 kowace shekara wanda aka yi 2009 kudaden da za bunkasa jami’oin Nijeriya.

  • Sin Da Amurka Sun Tsawaita Yarjejeniyar Hadin Gwiwa A Fannin Raya Kimiyya Da Fasaha Da Karin Shekaru 5
  • Bankin Duniya Da Hukumar Lamuni Ke Yi Wa Tsarin Ilimin Nijeriya Zagon-kasa – ASUU

Babban jami’in kungiyar da baya son a ambaci sunansa, ya bayyana cewa kungiyar ta shiryawa tafiya yajin aikin, muddin dai gwamnati ta ki sakin kudin saboda ayyukan da ake yi masu muhimmanci da suke karkashin kungiyar, shirye suke su fara yajin aiki idan har Shugaban kasa bai sa an bada kudaden ba.

Wata majiya tace matakin na, ASUU da har yanzu ba’a bayyana shi ba, ya tsaya kan rashin cika alkawarin da gwamnati ta yi na cika alkawarin da tayi tare da kungiyar a shekarar 2009 kan tsarin bukatunsu.Tsarin da aka dauka a matsayin mai canza al’amura wajen sake farfadowa da bunkasa abubuwan more rayuwa da za su taimakawa bunkasar ilimi a Jami’oin Nijeriya.

Majiyar ta ce shi shirin tafiya yajin aikin da za a yi ya dogara ne kan samun matsaya wadda ake sa ran cimmawa bayan taron da za a yi  na kwamitin zartarwa nan gaba bada dadewa ba.

Labarai Masu Nasaba

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

A wani ci gaban da aka samu wani babban kusa, na cibiyar kulawa da ayyuka ta jami’ar Jos Dr. Tunde Olagunjembi, wanda shi ne babban mai bincike ne, daga Jami’ar har ila yau kuma Malamin, ya ba Shugaban kasa shawarar kada ya yi watsi da  tsarin da aka fara wanda an yi shi ne, domin samar da kudade ga Jami’oin gwamnati saboda ci gabansu. Tsarin da aka fara an kirkiro shi ne domin a samu yin gyara kan abubuwan more rayuwa da suka lalace da kuma samar da kayan koyarwa a manyan makarantu.

Olagunjembi ya yi kira da Shugaban kasa ya ci gaba da tsarin da aka fara domin samun ci gaban yadda ake tafiyar da ilimin Jami’oi.

Ya yi kira da Shugaban kasa da kada ya bata lokaci ya amince saboda ci gaba na yin ayyukan, a makarantu da suke a karkashin tsarin.

Ya lashi takobin al’ummar Jami’a da kungiyar ASUU sun kosa da ganin yadda za a ci gaba da ayyukan a karkashin wannan mulkin.

Babban mai fada aji a Jami’a ya kara bayyana cewa samun dorewar karatu a makarantu hakan na faruwa ne sanadiyar sadaukar da kan da ‘yan kungiyar ta ASUU suka yi wadanda suka yanke shawarar za su ba Shugaban kasa lokaci domin ya samu damar tsai da hankalinsa kan ayyukan dake gabansa.

Sai dai kuma duk da hakan ya ja kunne cewar ruwa ya kusa karewa dan Kada,kamata ya yi Shugaban kasa ya dauki matakan da suka kamata wajen samar da kudade  don ci gaban ayyukan da aka fara.

Kamar yadda yace gabatar da, fara amfani samar da kudade saboda a samu aiwatar da tsarin yin ayyuka, hakan ta yiyu ne saboda yarjejeniyar da aka yi tsakanin gwamnatin tarayya da kungiyar ASUU, abin ya ta’allaka ne saboda ayi amfani da shawarwarin kwamitin ya bayar, domin ayi maganin matsalolin da ake fuskanta a manyan makarantu/ Jami’oin Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Jami'a
ShareTweetSendShare
Previous Post

Adadin Hatsin Da Kasar Sin Ta Samu A Bana Ya Haura Tan Miliyan 700 

Next Post

Nijeriya Za Ta Shiga Cikin Manyan Kasashe Masu Fitar Da Amfanin Gona A 2025 – Tinubu

Related

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?
Kasashen Ketare

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

8 hours ago
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025
Kasashen Ketare

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

10 hours ago
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17
Kasashen Ketare

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

22 hours ago
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
Ilimi

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

1 day ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

1 day ago
WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima
Ilimi

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

1 day ago
Next Post
Nijeriya Za Ta Shiga Cikin Manyan Kasashe Masu Fitar Da Amfanin Gona A 2025 – Tinubu

Nijeriya Za Ta Shiga Cikin Manyan Kasashe Masu Fitar Da Amfanin Gona A 2025 – Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.