• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Atiku Ga Tinubu: Fada Wa ‘Yan Nijeriya Yadda Ka Samu Digiri Ba Tare Da Firamare Da Sakandare Ba

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Atiku Ga Tinubu: Fada Wa ‘Yan Nijeriya Yadda Ka Samu Digiri Ba Tare Da Firamare Da Sakandare Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar, ya sake caccaki takardun makarantar Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu.

Atiku ya kalubalanci sahihancin takardar shaidar digirin Tinubu da jami’ar Chicago ta Amurka ta bayar, ya ce karatun shugaban kasar na ci gaba da zama babbar abun tantama.

  • Sakaci: Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Shugaban Asibitin Hasiya Bayero
  • Tottenham Da Chelsea Na Zawarcin Ansu Fati Na Barcelona

A wani sako da ya wallafa ta shafinsa na Tuwita, Atiku ya zargi shugaban kasar da kaurace kawo takardun karatunsa na firamare da sakandare amma sai ya kawo na digiri daga jami’ar Chicago.

A cewar tsohon mataimakin shugaban kasar, a shekarar 1999, Tinubu ya yi ikirarin cewa ya halarci makarantar firamare ta St. John’s da ke Aroloya a Legas, kafin ya wuce makarantar ‘Children’s Home’ da ke Ibadan.

Ya yi zargin cewa shaidar karatun Shugaba Tinubu a 2023 ya sha bamban da wanda aka gabatar a shekarar 1999, inda ya kara da cewa shugaban kasar ya ce ya halarci jami’ar Chicago ba tare da karatun firamare da sakandare ba.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

“Na farka da safiyar yau ina mamakin yadda muka sami wannan lamari. A cikin 1999, Tinubu ya yi ikirarin cewa ya halarci makarantar firamare ta St. John da ke Aroloya a Legas, kafin ya wuce zuwa makarantar ‘Children Home’ a Ibadan.”

“A cewarsa, ci gaba da karatu kwalejin gwamnati ta Ibadan da kwalejin Richard Daley da jami’ar Chicago ta Amurka.

“Abin mamakin shi ne, a 2023, Tinubu ya ce shi dai kwai ya halarci jami’ar Chicago kadai. Ina ta mamakin ko ta yaya hakan zai yiwu? Yana tunanin cewa ’yan Nijeriya ba za su shiga rudani ba kamar yadda na shiga cewa, Tinubu ba shi da takardar firamare da sakandare amma ya yi digiri a jami’a. Kuna iya tambayar Tinubu yadda ya samu wannan nasarar domin mu yi koyi da hazakarsa,” Atiku ya rubuta.

A watan Maris ne aka ayyana Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa na 2023. Amma Atiku ya ci gaba da kalubalantar sakamakon zaben a kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa, inda ya kalubalanci sahihancin takardun makarantar shugaban kasa.

Ya kuma garzaya wata kotun Amurka da ke gundumar Arewacin Jihar Illinois a Chicago, domin neman tilastawa jami’ar Chicago sakin bayanan karatun Tinubu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abinda Ya Kamata A Sani Game Da Jadawalin Gasar Kofin Zakarun Turai Na Bana 

Next Post

Goyon Bayan Da Amurka Ta Baiwa Japan Game Da Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Ba Shi Da Amfani

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

2 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

2 weeks ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

3 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

3 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

3 weeks ago
Next Post
Japan

Goyon Bayan Da Amurka Ta Baiwa Japan Game Da Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Ba Shi Da Amfani

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Atiku

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.