• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Atiku Ya Karbi Mutane Dubu 25 Da Suka Sauya Sheka Daga APC Zuwa PDP A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Atiku

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya misalta jam’iyyar a matsayin jam’iyya mai tasirin da za ta iya lashen 2023 da ke tafe. 

Atiku ya bayyana hakan a filin wasanni na Abubakar Tafawa Balewa, a ranar Laraba lokacin da ya karbi sama da mutum 25,000 da suka sauya sheka daga wasu jam’yyun zuwa PDP a Jihar Bauchi, ya misalta hakan a matsayin alamun nasara ga jam’iyyar.

  • Da Dumi-Dumi: ‘Yan Bindiga Sun Sako Ragowar Fasinjojin Jirgin Abuja-Kaduna 
  • NCCE Ta Garkame Kwalejojin Bogi 41 Da Ke Bayar da Shaidar NCE A Bauchi

“Yau kuma ga abun farin ciki ya same mu mun samu karuwa. Babu wani da zai zo ya yi hamayya da PDP a Bauchi ba wanda zai yi hamayya da Kauran Bauchi.”

Wazirin Adamawa, ya nuna kwarin guiwarsa da cewa dandanzon al’ummar da ya gani a wajen taron hakan ya nuna kyakkyawar alamar nasarar jam’iyyar a yayin zaben mai zuwa.

Daga bisani ya yi amfani da damar wajen jinjina wa kokarin gwamna Bala Muhammad na kyautata jihar tun lokacin da ya zama gwamna zuwa yanzu, “Muna taya ka murna da wannan kyakkyawan ci gaba da aka samu a Jihar Bauchi. Watannin baya da suka wuce na zo na kaddamar da wasu ayyyuka masu dumbin yawa wadanda ban taba gani a Bauchi ba sai a wannan karon a karkashin gwamantin Kauran Bauchi kuma a karkashin jam’iyyar PDP.

LABARAI MASU NASABA

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi

“Jama’ar Bauchi muna son mu dauki wannan damar mu taya ku murna domin yanzu kun samu gwamnati ta gari wacce ta ke kawo ci gaba a Jihar Bauchi.

“Amma ya kamata ku yi tunani cewa siyasar arewa daga nan Bauchi ta fara, nan ne cibiyar siyasa ta arewa don haka bai kamata ku rike siyasar PDP da bayan hannu ba.”

A nasa bangaren, gwamna Bala Muhammad na Jihar Bauchi kuma dan takarar gwamnan jihar a zaben 2023, ya nuna Atiku a matsayin hazikin da al’ummar Bauchi ke so a kowane lokaci kuma suka amince zai iya kai Nijeriya mataki na gaba.

“Muna tabbatar maka cewa mutanen Bauchi sun dawo suna tare da kai suna sonka kuma suna tare da mu. Muna gode musu saboda suna nuna kauna a gare mu bisa ayyukan da suka ga muna yi sakamakon dama da kuka ba mu. Kuma kai ka yi kokari a rayuwa, ka kasance mai taimakon mutane ka agaza musu.

“Kuma al’ummar Nijeriya sun san cewa idan ka zo, za ka taimaka ka azaga wa kowa.

“Ina tabbatar maka wadanda mutanen da ka gani naka ne. Kuma namu ne,” a cewarsa.

Gwamna Bala ya amshi bakoncin dan takarar shugaban kasa da abokin takararsa, Ifeanyi Okowa, shugaban jam’iyyar PDP na kasa Ayu Iyorchia, tare da sauran masu ruwa da tsaki a jam’iyyar.

Shi kuma shugaban jam’iyyar PDP reshen Jihar Bauchi, Hamza Koshe Akuyam, ya shaida cewar sama da mutum dubu ashirin da biyar da suka kunshi tsohon mataimakin gwamnan Jihar Bauchi da tsohon kakakin majalisar jihar ne suka saura sheka zuwa PDP.

Akuyam, ya ce irin dumbin jama’ar da suka fito domin tarbar Atiku da wadanda suka sauya sheka zuwa jam’iyyar sun yi bisa ganin dumbin ayyukan raya jihar da gwamantin PDP ta gudanar a jihar.

“Wadanda suka dawo wannan jam’iyyar sun dawo ne bisa ganin irin dumbin ayyukan da aka gudanar kuma gani suka yi ana abun kirki ana ayyukan da suka dace a Jihar Bauchi.

“Mutanen da ka karba yau sama da mutum dubu ashirin da biyar a cikinsu akwai tsohon mataimakin gwamnan Jihar Bauchi wanda ya sauka kwanan nan, akwai tsohon Kakakin Majalisa duk ‘yan jam’iyyar APC ne suka dawo cikin PDP.”

Shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Sanata Ayu Iyorchia, shi ne ya yi wankan shigo da wadanda suka sauya shekar zuwa PDP a jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan
Manyan Labarai

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

October 14, 2025
Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi
Siyasa

Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi

October 11, 2025
Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
Manyan Labarai

Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

October 11, 2025
Next Post
Mahakar Danyen Mai Ta Daqing Ta Samar Da Tan Biliyan 2.4

Mahakar Danyen Mai Ta Daqing Ta Samar Da Tan Biliyan 2.4

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

October 14, 2025
Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

October 14, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

October 14, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

October 14, 2025
Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

October 14, 2025
Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

October 13, 2025
Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.