• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Atiku Ya Karbi Mutane Dubu 25 Da Suka Sauya Sheka Daga APC Zuwa PDP A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Atiku

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya misalta jam’iyyar a matsayin jam’iyya mai tasirin da za ta iya lashen 2023 da ke tafe. 

Atiku ya bayyana hakan a filin wasanni na Abubakar Tafawa Balewa, a ranar Laraba lokacin da ya karbi sama da mutum 25,000 da suka sauya sheka daga wasu jam’yyun zuwa PDP a Jihar Bauchi, ya misalta hakan a matsayin alamun nasara ga jam’iyyar.

  • Da Dumi-Dumi: ‘Yan Bindiga Sun Sako Ragowar Fasinjojin Jirgin Abuja-Kaduna 
  • NCCE Ta Garkame Kwalejojin Bogi 41 Da Ke Bayar da Shaidar NCE A Bauchi

“Yau kuma ga abun farin ciki ya same mu mun samu karuwa. Babu wani da zai zo ya yi hamayya da PDP a Bauchi ba wanda zai yi hamayya da Kauran Bauchi.”

Wazirin Adamawa, ya nuna kwarin guiwarsa da cewa dandanzon al’ummar da ya gani a wajen taron hakan ya nuna kyakkyawar alamar nasarar jam’iyyar a yayin zaben mai zuwa.

Daga bisani ya yi amfani da damar wajen jinjina wa kokarin gwamna Bala Muhammad na kyautata jihar tun lokacin da ya zama gwamna zuwa yanzu, “Muna taya ka murna da wannan kyakkyawan ci gaba da aka samu a Jihar Bauchi. Watannin baya da suka wuce na zo na kaddamar da wasu ayyyuka masu dumbin yawa wadanda ban taba gani a Bauchi ba sai a wannan karon a karkashin gwamantin Kauran Bauchi kuma a karkashin jam’iyyar PDP.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Jama’ar Bauchi muna son mu dauki wannan damar mu taya ku murna domin yanzu kun samu gwamnati ta gari wacce ta ke kawo ci gaba a Jihar Bauchi.

“Amma ya kamata ku yi tunani cewa siyasar arewa daga nan Bauchi ta fara, nan ne cibiyar siyasa ta arewa don haka bai kamata ku rike siyasar PDP da bayan hannu ba.”

A nasa bangaren, gwamna Bala Muhammad na Jihar Bauchi kuma dan takarar gwamnan jihar a zaben 2023, ya nuna Atiku a matsayin hazikin da al’ummar Bauchi ke so a kowane lokaci kuma suka amince zai iya kai Nijeriya mataki na gaba.

“Muna tabbatar maka cewa mutanen Bauchi sun dawo suna tare da kai suna sonka kuma suna tare da mu. Muna gode musu saboda suna nuna kauna a gare mu bisa ayyukan da suka ga muna yi sakamakon dama da kuka ba mu. Kuma kai ka yi kokari a rayuwa, ka kasance mai taimakon mutane ka agaza musu.

“Kuma al’ummar Nijeriya sun san cewa idan ka zo, za ka taimaka ka azaga wa kowa.

“Ina tabbatar maka wadanda mutanen da ka gani naka ne. Kuma namu ne,” a cewarsa.

Gwamna Bala ya amshi bakoncin dan takarar shugaban kasa da abokin takararsa, Ifeanyi Okowa, shugaban jam’iyyar PDP na kasa Ayu Iyorchia, tare da sauran masu ruwa da tsaki a jam’iyyar.

Shi kuma shugaban jam’iyyar PDP reshen Jihar Bauchi, Hamza Koshe Akuyam, ya shaida cewar sama da mutum dubu ashirin da biyar da suka kunshi tsohon mataimakin gwamnan Jihar Bauchi da tsohon kakakin majalisar jihar ne suka saura sheka zuwa PDP.

Akuyam, ya ce irin dumbin jama’ar da suka fito domin tarbar Atiku da wadanda suka sauya sheka zuwa jam’iyyar sun yi bisa ganin dumbin ayyukan raya jihar da gwamantin PDP ta gudanar a jihar.

“Wadanda suka dawo wannan jam’iyyar sun dawo ne bisa ganin irin dumbin ayyukan da aka gudanar kuma gani suka yi ana abun kirki ana ayyukan da suka dace a Jihar Bauchi.

“Mutanen da ka karba yau sama da mutum dubu ashirin da biyar a cikinsu akwai tsohon mataimakin gwamnan Jihar Bauchi wanda ya sauka kwanan nan, akwai tsohon Kakakin Majalisa duk ‘yan jam’iyyar APC ne suka dawo cikin PDP.”

Shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Sanata Ayu Iyorchia, shi ne ya yi wankan shigo da wadanda suka sauya shekar zuwa PDP a jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
Siyasa

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
Mahakar Danyen Mai Ta Daqing Ta Samar Da Tan Biliyan 2.4

Mahakar Danyen Mai Ta Daqing Ta Samar Da Tan Biliyan 2.4

LABARAI MASU NASABA

An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

November 7, 2025

Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho

November 7, 2025
Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025
Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

November 7, 2025
An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.