• English
  • Business News
Sunday, July 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Atiku Ya Karbi Mutane Dubu 25 Da Suka Sauya Sheka Daga APC Zuwa PDP A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Siyasa
0
Atiku Ya Karbi Mutane Dubu 25 Da Suka Sauya Sheka Daga APC Zuwa PDP A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya misalta jam’iyyar a matsayin jam’iyya mai tasirin da za ta iya lashen 2023 da ke tafe. 

Atiku ya bayyana hakan a filin wasanni na Abubakar Tafawa Balewa, a ranar Laraba lokacin da ya karbi sama da mutum 25,000 da suka sauya sheka daga wasu jam’yyun zuwa PDP a Jihar Bauchi, ya misalta hakan a matsayin alamun nasara ga jam’iyyar.

  • Da Dumi-Dumi: ‘Yan Bindiga Sun Sako Ragowar Fasinjojin Jirgin Abuja-Kaduna 
  • NCCE Ta Garkame Kwalejojin Bogi 41 Da Ke Bayar da Shaidar NCE A Bauchi

“Yau kuma ga abun farin ciki ya same mu mun samu karuwa. Babu wani da zai zo ya yi hamayya da PDP a Bauchi ba wanda zai yi hamayya da Kauran Bauchi.”

Wazirin Adamawa, ya nuna kwarin guiwarsa da cewa dandanzon al’ummar da ya gani a wajen taron hakan ya nuna kyakkyawar alamar nasarar jam’iyyar a yayin zaben mai zuwa.

Daga bisani ya yi amfani da damar wajen jinjina wa kokarin gwamna Bala Muhammad na kyautata jihar tun lokacin da ya zama gwamna zuwa yanzu, “Muna taya ka murna da wannan kyakkyawan ci gaba da aka samu a Jihar Bauchi. Watannin baya da suka wuce na zo na kaddamar da wasu ayyyuka masu dumbin yawa wadanda ban taba gani a Bauchi ba sai a wannan karon a karkashin gwamantin Kauran Bauchi kuma a karkashin jam’iyyar PDP.

Labarai Masu Nasaba

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

“Jama’ar Bauchi muna son mu dauki wannan damar mu taya ku murna domin yanzu kun samu gwamnati ta gari wacce ta ke kawo ci gaba a Jihar Bauchi.

“Amma ya kamata ku yi tunani cewa siyasar arewa daga nan Bauchi ta fara, nan ne cibiyar siyasa ta arewa don haka bai kamata ku rike siyasar PDP da bayan hannu ba.”

A nasa bangaren, gwamna Bala Muhammad na Jihar Bauchi kuma dan takarar gwamnan jihar a zaben 2023, ya nuna Atiku a matsayin hazikin da al’ummar Bauchi ke so a kowane lokaci kuma suka amince zai iya kai Nijeriya mataki na gaba.

“Muna tabbatar maka cewa mutanen Bauchi sun dawo suna tare da kai suna sonka kuma suna tare da mu. Muna gode musu saboda suna nuna kauna a gare mu bisa ayyukan da suka ga muna yi sakamakon dama da kuka ba mu. Kuma kai ka yi kokari a rayuwa, ka kasance mai taimakon mutane ka agaza musu.

“Kuma al’ummar Nijeriya sun san cewa idan ka zo, za ka taimaka ka azaga wa kowa.

“Ina tabbatar maka wadanda mutanen da ka gani naka ne. Kuma namu ne,” a cewarsa.

Gwamna Bala ya amshi bakoncin dan takarar shugaban kasa da abokin takararsa, Ifeanyi Okowa, shugaban jam’iyyar PDP na kasa Ayu Iyorchia, tare da sauran masu ruwa da tsaki a jam’iyyar.

Shi kuma shugaban jam’iyyar PDP reshen Jihar Bauchi, Hamza Koshe Akuyam, ya shaida cewar sama da mutum dubu ashirin da biyar da suka kunshi tsohon mataimakin gwamnan Jihar Bauchi da tsohon kakakin majalisar jihar ne suka saura sheka zuwa PDP.

Akuyam, ya ce irin dumbin jama’ar da suka fito domin tarbar Atiku da wadanda suka sauya sheka zuwa jam’iyyar sun yi bisa ganin dumbin ayyukan raya jihar da gwamantin PDP ta gudanar a jihar.

“Wadanda suka dawo wannan jam’iyyar sun dawo ne bisa ganin irin dumbin ayyukan da aka gudanar kuma gani suka yi ana abun kirki ana ayyukan da suka dace a Jihar Bauchi.

“Mutanen da ka karba yau sama da mutum dubu ashirin da biyar a cikinsu akwai tsohon mataimakin gwamnan Jihar Bauchi wanda ya sauka kwanan nan, akwai tsohon Kakakin Majalisa duk ‘yan jam’iyyar APC ne suka dawo cikin PDP.”

Shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Sanata Ayu Iyorchia, shi ne ya yi wankan shigo da wadanda suka sauya shekar zuwa PDP a jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCAtikuAyuBauchiKauran BauchiPDPSauya Sheka
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ranar Malamai ta Duniya: Atiku Ya Bukaci A Yi Wa Ilimi Tagomashi

Next Post

Mahakar Danyen Mai Ta Daqing Ta Samar Da Tan Biliyan 2.4

Related

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

4 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

11 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

15 hours ago
Ba A Taɓa Nuno Bidiyon Shugaban Jam’iyyarmu Ta ADC Yana Cusa Dala A Aljihu Ba —Dalung
Labarai

Ba A Taɓa Nuno Bidiyon Shugaban Jam’iyyarmu Ta ADC Yana Cusa Dala A Aljihu Ba —Dalung

2 days ago
‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

2 days ago
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC
Siyasa

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

2 days ago
Next Post
Mahakar Danyen Mai Ta Daqing Ta Samar Da Tan Biliyan 2.4

Mahakar Danyen Mai Ta Daqing Ta Samar Da Tan Biliyan 2.4

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

July 5, 2025
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

July 5, 2025
‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

July 5, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

July 5, 2025
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.