ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Atiku Ya Karbi Mutane Dubu 25 Da Suka Sauya Sheka Daga APC Zuwa PDP A Bauchi

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Atiku

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya misalta jam’iyyar a matsayin jam’iyya mai tasirin da za ta iya lashen 2023 da ke tafe. 

Atiku ya bayyana hakan a filin wasanni na Abubakar Tafawa Balewa, a ranar Laraba lokacin da ya karbi sama da mutum 25,000 da suka sauya sheka daga wasu jam’yyun zuwa PDP a Jihar Bauchi, ya misalta hakan a matsayin alamun nasara ga jam’iyyar.

  • Da Dumi-Dumi: ‘Yan Bindiga Sun Sako Ragowar Fasinjojin Jirgin Abuja-Kaduna 
  • NCCE Ta Garkame Kwalejojin Bogi 41 Da Ke Bayar da Shaidar NCE A Bauchi

“Yau kuma ga abun farin ciki ya same mu mun samu karuwa. Babu wani da zai zo ya yi hamayya da PDP a Bauchi ba wanda zai yi hamayya da Kauran Bauchi.”

ADVERTISEMENT

Wazirin Adamawa, ya nuna kwarin guiwarsa da cewa dandanzon al’ummar da ya gani a wajen taron hakan ya nuna kyakkyawar alamar nasarar jam’iyyar a yayin zaben mai zuwa.

Daga bisani ya yi amfani da damar wajen jinjina wa kokarin gwamna Bala Muhammad na kyautata jihar tun lokacin da ya zama gwamna zuwa yanzu, “Muna taya ka murna da wannan kyakkyawan ci gaba da aka samu a Jihar Bauchi. Watannin baya da suka wuce na zo na kaddamar da wasu ayyyuka masu dumbin yawa wadanda ban taba gani a Bauchi ba sai a wannan karon a karkashin gwamantin Kauran Bauchi kuma a karkashin jam’iyyar PDP.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

“Jama’ar Bauchi muna son mu dauki wannan damar mu taya ku murna domin yanzu kun samu gwamnati ta gari wacce ta ke kawo ci gaba a Jihar Bauchi.

“Amma ya kamata ku yi tunani cewa siyasar arewa daga nan Bauchi ta fara, nan ne cibiyar siyasa ta arewa don haka bai kamata ku rike siyasar PDP da bayan hannu ba.”

A nasa bangaren, gwamna Bala Muhammad na Jihar Bauchi kuma dan takarar gwamnan jihar a zaben 2023, ya nuna Atiku a matsayin hazikin da al’ummar Bauchi ke so a kowane lokaci kuma suka amince zai iya kai Nijeriya mataki na gaba.

“Muna tabbatar maka cewa mutanen Bauchi sun dawo suna tare da kai suna sonka kuma suna tare da mu. Muna gode musu saboda suna nuna kauna a gare mu bisa ayyukan da suka ga muna yi sakamakon dama da kuka ba mu. Kuma kai ka yi kokari a rayuwa, ka kasance mai taimakon mutane ka agaza musu.

“Kuma al’ummar Nijeriya sun san cewa idan ka zo, za ka taimaka ka azaga wa kowa.

“Ina tabbatar maka wadanda mutanen da ka gani naka ne. Kuma namu ne,” a cewarsa.

Gwamna Bala ya amshi bakoncin dan takarar shugaban kasa da abokin takararsa, Ifeanyi Okowa, shugaban jam’iyyar PDP na kasa Ayu Iyorchia, tare da sauran masu ruwa da tsaki a jam’iyyar.

Shi kuma shugaban jam’iyyar PDP reshen Jihar Bauchi, Hamza Koshe Akuyam, ya shaida cewar sama da mutum dubu ashirin da biyar da suka kunshi tsohon mataimakin gwamnan Jihar Bauchi da tsohon kakakin majalisar jihar ne suka saura sheka zuwa PDP.

Akuyam, ya ce irin dumbin jama’ar da suka fito domin tarbar Atiku da wadanda suka sauya sheka zuwa jam’iyyar sun yi bisa ganin dumbin ayyukan raya jihar da gwamantin PDP ta gudanar a jihar.

“Wadanda suka dawo wannan jam’iyyar sun dawo ne bisa ganin irin dumbin ayyukan da aka gudanar kuma gani suka yi ana abun kirki ana ayyukan da suka dace a Jihar Bauchi.

“Mutanen da ka karba yau sama da mutum dubu ashirin da biyar a cikinsu akwai tsohon mataimakin gwamnan Jihar Bauchi wanda ya sauka kwanan nan, akwai tsohon Kakakin Majalisa duk ‘yan jam’iyyar APC ne suka dawo cikin PDP.”

Shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Sanata Ayu Iyorchia, shi ne ya yi wankan shigo da wadanda suka sauya shekar zuwa PDP a jihar.

Atiku
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Mahakar Danyen Mai Ta Daqing Ta Samar Da Tan Biliyan 2.4

Mahakar Danyen Mai Ta Daqing Ta Samar Da Tan Biliyan 2.4

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.